< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Glasno prepevajte Bogu, naši môči, naredite radosten glas Jakobovemu Bogu.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Vzemite psalm in prinesite sèm tamburin, prijetno harfo s plunko.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Trobite na šofar ob mlaju, ob določenem času na naš slovesni praznični dan.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Kajti to je bil zakon za Izraela in postava Jakobovega Boga.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
To je odredil v Jožefu za pričevanje, ko je šel ven skozi egiptovsko deželo, kjer sem slišal jezik, ki ga nisem razumel:
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
»Njegovo ramo sem odstranil od bremena, njegove roke so bile osvobojene pred lonci.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Ti kličeš v stiski in jaz sem te osvobodil, odgovoril sem ti na skrivnem kraju groma. Jaz sem te preizkusil pri vodah Meríbe. (Sela)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Poslušaj, oh moje ljudstvo, pričeval ti bom, oh Izrael, če bi mi hotel prisluhniti.
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
V tebi naj ne bo tujega boga niti ne boš oboževal nobenega tujega boga.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Jaz sem Gospod, tvoj Bog, ki te je privedel iz egiptovske dežele. Široko odpri svoja usta in napolnil jih bom.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Toda moje ljudstvo noče prisluhniti mojemu glasu in Izrael noče ničesar od mene.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Tako sem jih izročil njihovim lastnim srčnim željam in živeli so po svojih lastnih nasvetih.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Oh, da bi mi moje ljudstvo prisluhnilo in bi Izrael hodil po mojih poteh!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Kmalu bi podjarmil njihove sovražnike in svojo roko obrnil zoper njihove nasprotnike.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Gospodovi sovražniki bi se morali podvreči pod njega, pa bi se njihov čas ohranil na veke.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Hranil bi jih tudi z najodličnejšo pšenico in z medom iz skale bi te nasitil.«

< Zabura 81 >