< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
В конец, о точилех, псалом Асафу. Радуйтеся Богу помощнику нашему, воскликните Богу Иаковлю:
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
приимите псалом и дадите тимпан, псалтирь красен с гусльми:
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
вострубите в новомесячии трубою, во благознаменитый день праздника вашего:
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
яко повеление Израилеви есть, и судба Богу Иаковлю.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Свидение во Иосифе положи е, внегда изыти ему от земли Египетския: языка, егоже не ведяше, услыша.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
Отят от бремене хребет его: руце его в коши поработасте.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
В скорби призвал Мя еси, и избавих тя: услышах тя в тайне бурне: искусих тя на воде Пререкания.
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Слышите, людие Мои, и засвидетелствую вам, Израилю, аще послушаеши Мене:
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
не будет тебе бог нов, ниже поклонишися богу чуждему.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Аз бо есмь Господь Бог твой, изведый тя от земли Египетския: разшири уста твоя, и исполню я.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
И не послушаша людие Мои гласа Моего, и Израиль не внят Ми:
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
и отпустих я по начинанием сердец их, пойдут в начинаниих своих.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Аще быша людие Мои послушали Мене, Израиль аще бы в пути Моя ходил:
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
ни о чесомже убо враги его смирил бых, и на оскорбляющыя их возложил бых руку Мою.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Врази Господни солгаша ему, и будет время их в век:
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
и напита их от тука пшенична, и от камене меда насыти их.

< Zabura 81 >