< Zabura 81 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Salmo de Asafe, para o regente, conforme “Gitite”: Cantai de alegria a Deus, [que é] nossa força; mostrai alegria ao Deus de Jacó.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Levantai uma canção, e dai-nos o tamborim; a agradável harpa com a lira.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Tocai trombeta na lua nova; e na lua cheia, no dia de nossa celebração.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Porque [isto] é um estatuto em Israel, e uma ordem do Deus de Jacó.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Ele o pôs como testemunho em José, quando tinha saído contra a terra do Egito, [onde] ouvi uma língua que eu não entendia:
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
Tirei seus ombros de debaixo da carga; suas mãos foram livrados dos cestos.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Na angústia clamaste, e livrei-te dela; te respondi no esconderijo dos trovões; provei a ti nas águas de Meribá. (Selá)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Ouve [-me], povo meu, e eu te darei testemunho; ó Israel, se tu me ouvisses!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Não haverá entre ti deus estranho, e não te prostrarás a um deus estrangeiro.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Eu sou o SENHOR teu Deus, que te fiz subir da terra do Egito; abre tua boca por completo, e eu a encherei.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Mas meu povo não ouviu minha voz, e Israel não me quis.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Por isso eu os entreguei ao desejo de seus próprios corações, e andaram conforme seus próprios conselhos.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Ah, se meu povo me ouvisse, se Israel andasse em meus caminhos!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Em pouco tempo eu derrotaria seus inimigos, e viraria minha mão contra seus adversários.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Os que odeiam ao SENHOR, a ele se submeteriam, e o tempo [da punição] deles seria eterno.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
E ele sustentaria [Israel] com a abundância de trigo; e eu te fartaria com o mel da rocha.