< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Dem Sangmeister, auf der Gittit. Von Asaf.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
(Der levitische Sängerchor: ) / Laßt Jubel erschallen Elohim, unserm Hort, / Jauchzet dem Gotte Jakobs!
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Stimmt an Gesang, laßt tönen die Pauke, / Die liebliche Zither und Harfe!
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Blaset am Neumond das Widderhorn, / Beim Vollmond, für unsern Feiertag!
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Denn so ist es Satzung für Israel, / Eine Vorschrift des Gottes Jakobs.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
Als Gebot hat er's für Josef bestimmt, / Da er auszog wider Ägyptenland. / (Eine Einzelstimme: ) / Eine Sprache, mir fremd, vernehm ich:
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
"Seinen Nacken hab ich von der Bürde befreit, / Seine Hände wurden des Lastkorbs ledig.
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Du riefst in der Not, ich riß dich heraus, / Erhörte dich aus Gewittergewölk, / Prüfte dich an Meribas Wassern. (Sela)
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Höre, mein Volk, ich will dich warnen! / Israel, möchtest du mir gehorchen!
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Nicht sei unter dir ein fremder Gott; / Bete nicht an einen Gott des Auslands!
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Ich, Jahwe, bin dein Gott, / Der dich geführt aus Ägyptenland: / Tu deinen Mund weit auf, / Damit ich ihn fülle!
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Aber mein Volk gehorchte mir nicht, / Israel war mir nicht zu Willen.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Da stieß ich sie weg, weil ihr Herz so verstockt, / Daß sie folgten den eignen Gedanken.
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
O daß doch mein Volk mir gehorchte, / Daß Israel ginge auf meinen Wegen!
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Wie leicht könnt ich da ihre Feinde beugen, / Meine Hand gegen ihre Dränger kehren.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Ihnen müßten schmeicheln, die Jahwe hassen, / Und ewig würde währen ihr Glück. Mit dem besten Weizen würd ich sie speisen, / Mit Honig aus Felsen dich sättigen."

< Zabura 81 >