< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Pour les pressoirs, psaume d’Asaph lui-même. Exultez en Dieu qui est notre aide; poussez des cris de joie vers le Dieu de Jacob.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Entonnez un psaume, et faites entendre un tambour, un psaltérion harmonieux avec une harpe.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Sonnez de la trompette à la néoménie, au jour insigne de votre solennité;
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Parce que c’est un précepte dans Israël, une ordonnance en l’honneur du Dieu de Jacob.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Il l’établit comme un monument pour Joseph, lorsqu’il sortit de la terre d’Égypte, et qu’il entendit une langue qu’il ne connaissait pas.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
Il détourna son dos des fardeaux, et ses mains qui servaient à porter les corbeilles.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Dans la tribulation, tu m’as invoqué, et je t’ai délivré; je t’ai exaucé du fond de la tempête, je t’ai éprouvé auprès de l’eau de contradiction.
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Écoute, mon peuple, car je te prendrai à témoin: Israël, si tu m’écoutes,
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Il n’y aura pas au milieu de toi de dieu nouveau, et tu n’adoreras pas de dieu étranger.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Car c’est moi qui suis le Seigneur ton Dieu, qui t’ai tiré de la terre d’Égypte; élargis la bouche, je la remplirai.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Mais mon peuple n’a pas écouté ma voix, et Israël ne m’a pas prêté attention.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Et je les ai abandonnés aux désirs de leur cœur; ils iront dans des voies de leur invention.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Si mon peuple m’avait écouté; si Israël avait marché dans mes voies,
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
En un moment j’aurais humilié ses ennemis, et sur ceux qui les tourmentaient, j’aurais lancé ma main.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Les ennemis du Seigneur lui ont menti, et leur temps durera des siècles.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Cependant il les a nourris de moelle de froment, et il les a rassasiés de miel sorti d’une pierre.

< Zabura 81 >