< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
To the chief Musician upon Gittith, [A Psalm] of Asaph. Sing aloud to God our strength: make a joyful noise to the God of Jacob.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Take a psalm, and bring hither the timbrel, the pleasant harp with the psaltery.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Blow the trumpet in the new moon, in the time appointed, on our solemn feast day.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
For this [was] a statute for Israel, [and] a law of the God of Jacob.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
This he ordained in Joseph [for] a testimony, when he went out through the land of Egypt: [where] I heard a language [that] I understood not.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
I removed his shoulder from the burden: his hands were delivered from the pots.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Thou calledst in trouble, and I delivered thee; I answered thee in the secret place of thunder: I proved thee at the waters of Meribah. (Selah)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Hear, O my people, and I will testify to thee; O Israel, if thou wilt hearken to me;
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
There shall no strange god be in thee; neither shalt thou worship any strange god.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
I [am] the LORD thy God who brought thee out of the land of Egypt: open thy mouth wide, and I will fill it.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
But my people would not hearken to my voice; and Israel would not obey me.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
So I gave them up to their own hearts lust: [and] they walked in their own counsels.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
O that my people had hearkened to me, [and] Israel had walked in my ways!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
I should soon have subdued their enemies, and turned my hand against their adversaries.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
The haters of the LORD should have submitted themselves to him: and their time should have endured for ever.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
He would have fed them also with the finest of the wheat: and with honey out of the rock I should have satisfied thee.

< Zabura 81 >