< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
To the choirmaster - on the Gittith of Asaph. Sing for joy to God strength our shout for joy to [the] God of Jacob.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Lift up music and beat a tambourine a harp pleasant with a lyre.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Blow at the new moon a ram's horn at the full moon to [the] day of festival our.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
For [is] a decree for Israel it an ordinance of [the] God of Jacob.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
A testimony - in Joseph he established it when went out he on [the] land of Egypt a language [which] not I knew I heard.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
I removed from a burden shoulder his hands his from a basket they passed away.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
In trouble you called out and I rescued you I answered you in [the] hiding place of thunder I tested you at [the] waters of Meribah (Selah)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Listen O people my so let me warn you O Israel if you will listen to me.
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Not it will be among you a god strange and not you must bow down to a god of foreignness.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
I - [am] Yahweh God your who brought up you from [the] land of Egypt make large mouth your and I will fill it.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
And not it listened people my to voice my and Israel not it yielded to me.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
And I gave over it in [the] stubbornness of heart their they walked in own schemes their.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
If people my [will be] listening to me Israel in ways my they will walk.
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Like a little enemies their I will subdue and on opponents their I will turn hand my.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
[those who] hate Yahweh They will cringe to him and may it be time their for ever.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
And he fed him from [the] best of [the] wheat and from a rock honey I will satisfy you.

< Zabura 81 >