< Zabura 81 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
“To the chief musician upon Gittith; by Assaph.” Sing aloud unto God our strength: shout joyfully unto the God of Jacob.
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Lift up psalm, and bring hither the timbrel, the pleasant harp with the psaltery.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Blow on the new moon the cornet, at the time appointed, on the day of our feast.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
For this is a statute for Israel, an ordinance by the God of Jacob.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
As a testimony in Joseph did he ordain it, when he went out over the land of Egypt. The language of one I had not known did I hear.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
I removed from the burden his shoulder: his hands left behind the burden-basket.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
In distress thou didst call, and I delivered thee; I answered thee in the secret of the thunder: I proved thee at the waters of Meribah. (Selah)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Hear, O my people, and I will give warning unto thee; O Israel, if thou wouldst but hearken unto me!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
There shall not be among thee a foreign God; nor shalt thou bow thyself down to any strange God.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
I am the Lord thy God, who have brought thee up out of the land of Egypt: open wide thy mouth, and I will fill it.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
But my people did not hearken to my voice; and Israel was not willing [to follow] me.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
So I let them go in the stubbornness of their own hearts: and they walked in their own counsels.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Oh that my people would hearken unto me, that Israel would walk in my ways!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
In a little while would I subdue their enemies, and against their adversaries would I turn my hand.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
The haters of the Lord should offer flattery unto him; but their time should endure for ever.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
And he would feed him with the best of wheat: and out of the rock would I satisfy thee with honey.