< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Voor muziekbegeleiding; op de gittiet. Van Asaf. Jubelt voor God, onze sterkte, Juicht den God van Jakob ter eer;
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Stemt lofzangen aan, slaat de pauken, Met lieflijke citer en harp;
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Steekt deze maand de bazuinen, Bij volle maan voor de dag van ons feest!
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Want dit is een voorschrift aan Israël, En een bevel van Jakobs God:
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Een gebod, aan Josef gegeven, Na zijn tocht uit het land van Egypte, Toen hij een woord vernam, Dat hij nooit had gehoord:
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
Ik heb de last van uw schouders genomen, En uw handen werden van de draagkorf bevrijd.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Gij riept in de nood, En Ik heb u verlost, In donderwolken u verhoord, Bij de wateren van Meriba u beproefd.
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Hoor, mijn volk, Ik ga het u plechtig verkonden; Israël, ach, luister naar Mij:
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Geen andere god mag er onder u zijn; Geen vreemden god moogt gij aanbidden!
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Ik ben Jahweh, uw God, die u uit Egypte heb geleid, En die uw mond heb gevuld, toen hij wijd was geopend!
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Maar mijn volk luisterde niet naar mijn stem, En Israël gehoorzaamde niet;
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Toen gaf ik ze prijs aan verstoktheid des harten, En iedereen ging zijn eigen weg.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Ach, had mijn volk naar Mij toch geluisterd, En Israël mijn wegen bewandeld!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Hoe snel had Ik dan zijn vijand vernederd, Mijn hand op zijn verdrukkers doen komen;
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Al hadden Jahweh’s haters Hem nog zo gevleid, Hun tijd was voor eeuwig gekomen!
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Maar u zou Ik spijzen met de bloem van de tarwe, En verzadigen met honing uit de rotsen.

< Zabura 81 >