< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Kuom jatend wer. Wer mower kaluwore gi Gitith. Mar Asaf. Weruru matek gi mor ne Nyasaye mamiyowa teko, gouru koko matek ne Nyasach Jakobo!
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Chakuru wer, yiekuru oyieke; gweluru nyatiti gi asili mamit.
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
Gouru tung im ka dwe manyien ochakore, ma en ka dwe osetegno, e odiechiengʼ mar Nyasiwa mogen.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Ma en gima ochuno jo-Israel; chik ma Nyasach Jakobo nogolo.
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
Kane Nyasaye mirima omako gi jo-Misri, to ne ogure kaka chik ne Josef. Ne awinjo dwol ma ok angʼeyo kuma oaye kawacho kama:
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
“Ne agolo tingʼ mapek e gokgi, mi lwetgi nogony e tingʼo atonge.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Ne iluongo ka in e chandruok mi akonyi, ne adwoki gi ei boche polo, kendo ne atemi e tie pige mag Meriba. (Sela)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
“Winjuru wach, yaye joga, to abiro siemou, abiro siemou ka uikoru mar winja, yaye Israel.
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Kik ubed gi nyasaye ma wendo e dieru, kendo kik ukulru ne nyasaye ma ukia.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
An Jehova Nyasaye, ma Nyasachu, mane ogolou Misri. Ngʼamuru dhou malach mondo apongʼe.
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
“To joga nodagi winjo dwonda kendo Israel nodagi timo kaka achikogi.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Omiyo ne aweyogi nikech chunygi ne tek, kendo negiluwo yoregi giwegi.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
“Ka dine joga yie winja, ka dine Israel yie lu yorena,
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
mano kaka dine atieko wasikgi piyo piyo kendo dine agoyo joma kedo kodgi gi lweta!
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Joma ochayo Jehova Nyasaye dine okulorene gi luoro, kendo kum margi osiko nyaka chiengʼ.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
To un dine apidhou gi ngano maber mogik, kendo dine aromou gi mor kich ma athodho e lwanda.”

< Zabura 81 >