< Zabura 81 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
(Til Sangmesteren. Al-haggittit. Af Asaf.) Jubler for Gud, vor Styrke, råb af fryd for Jakobs Gud,
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
istem Lovsang, lad Pauken lyde, den liflige Citer og Harpen;
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
stød i Hornet på Nymånedagen, ved Fuldmåneskin på vor Højtidsdag!
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Thi det er Lov i Israel, et Bud fra Jakobs Gud;
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
han gjorde det til en Vedtægt i Josef, da han drog ud fra Ægypten, hvor han hørte et Sprog, han ikke kendte.
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
"Jeg fried hans Skulder for Byrden, hans Hænder slap fri for Kurven.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
I Nøden råbte du, og jeg frelste dig, jeg svarede dig i Tordenens Skjul, jeg prøvede dig ved Meribas Vande. (Sela)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
Hør, mit Folk, jeg vil vidne for dig, Israel, ak, om du hørte mig!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
En fremmed Gud må ej findes hos dig, tilbed ikke andres Gud!
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Jeg, HERREN, jeg er din Gud! som førte dig op fra Ægypten; luk din Mund vidt op, og jeg vil fylde den!
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Men mit Folk vilde ikke høre min Røst, Israel lød mig ikke.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Da lod jeg dem fare i deres Stivsind, de vandrede efter deres egne Råd.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Ak, vilde mit Folk dog høre mig, Israel gå mine Veje!
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
Da kued jeg snart deres Fjender, vendte min Hånd mod deres Uvenner!
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Deres Avindsmænd skulde falde og gå til Grunde for evigt;
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
jeg nærede dig med Hvedens Fedme, mættede dig med Honning fra Klippen!"

< Zabura 81 >