< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Kwa mwimbishaji. Mtindo wa “Yungiyungi za Agano.” Zaburi ya Asafu. Ee Mchungaji wa Israeli tusikie, wewe umwongozaye Yosefu kama kundi; wewe uketiye katika kiti cha enzi katikati ya makerubi, angaza
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
mbele ya Efraimu, Benyamini na Manase. Uamshe nguvu zako, uje utuokoe.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Ee Mungu, uturejeshe, utuangazie uso wako, ili tuweze kuokolewa.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Ee Bwana Mungu Mwenye Nguvu Zote, hata lini hasira yako itawaka na kufoka moshi dhidi ya maombi ya watu wako?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Umewalisha kwa mkate wa machozi, umewafanya wanywe machozi bakuli tele.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Tumekuwa chanzo cha ugomvi kwa jirani zetu, na adui zetu wanatudhihaki.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Ee Mungu Mwenye Nguvu Zote, uturejeshe; utuangazie uso wako, nasi tuweze kuokolewa.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Ulileta mzabibu kutoka Misri, ukawafukuza mataifa, ukaupanda.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Uliandaa shamba kwa ajili yake, mizizi ikawa imara, ukajaza nchi.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Milima ilifunikwa kwa kivuli chake, matawi yake yakafunika mierezi mikubwa.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Matawi yake yalienea mpaka Baharini, machipukizi yake mpaka kwenye Mto.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Mbona umebomoa kuta zake ili wote wapitao karibu wazichume zabibu zake?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Nguruwe mwitu wanauharibu na wanyama wa kondeni hujilisha humo.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Turudie, Ee Mungu Mwenye Nguvu Zote! Tazama chini kutoka mbinguni na uone! Linda mzabibu huu,
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
mche ulioupanda kwa mkono wako wa kuume, mwana uliyemlea kwa ajili yako mwenyewe.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Mzabibu wako umekatwa, umechomwa moto, unapowakemea, watu wako huangamia.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Mkono wako na utulie juu ya mtu aliyeko mkono wako wa kuume, mwana wa mtu uliyemlea kwa ajili yako mwenyewe.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Ndipo hatutakuacha tena, utuhuishe, nasi tutaliitia jina lako.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Ee Bwana Mungu Mwenye Nguvu Zote, uturejeshe; utuangazie uso wako, ili tuweze kuokolewa.

< Zabura 80 >