< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Al Vencedor: sobre Sosanim: testimonio de Asaf: Salmo. Oh Pastor de Israel, escucha; tú que pastoreas como a ovejas a José, que estás entre querubines, resplandece.
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Despierta tu valentía delante de Efraín, y de Benjamín, y de Manasés, y ven a salvarnos.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Oh Dios, haznos tornar; y haz resplandecer tu rostro, y seremos salvos.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
SEÑOR, Dios de los ejércitos, ¿Hasta cuándo humearás tú contra la oración de tu pueblo?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Les diste a comer pan de lágrimas, y les diste a beber lágrimas con medida.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Nos pusiste por contienda a nuestros vecinos; y nuestros enemigos se burlan de nosotros entre sí.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Oh Dios de los ejércitos, haznos tornar; y haz resplandecer tu rostro, y seremos salvos.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Hiciste venir una vid desde Egipto; echaste los gentiles, y la plantaste.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Limpiaste sitio delante de ella, e hiciste arraigar sus raíces, y llenó la tierra.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Los montes fueron cubiertos de su sombra; y sus ramas como cedros de Dios.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Envió sus ramas hasta el mar, y hasta el río sus renuevos.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
¿Por qué aportillaste sus vallados, y la vendimian todos los que pasan por el camino?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
La estropeó el puerco montés, y la pació la bestia del campo.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Oh Dios de los ejércitos, vuelve ahora; mira desde el cielo, y ve, y visita esta vid,
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
y la viña que tu diestra plantó, y sobre el renuevo que corroboraste para ti.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Quemada a fuego está, y talada; perezcan por la reprensión de tu rostro.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Sea tu mano sobre el varón de tu diestra, sobre el hijo del hombre que corroboraste para ti.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Así no nos volveremos de ti; nos darás vida, e invocaremos tu Nombre.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Oh SEÑOR, Dios de los ejércitos, haznos tornar; haz resplandecer tu rostro, y seremos salvos.