< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Načelniku godbe na šestero strun: psalm pričanja Asafu. O pastir Izraelov, poslušaj, ki vodiš Jožefa kakor čedo, sedeč na Kerubih prisvéti!
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Pred Efrajmom, Benjaminom in Manasom zbudi moč svojo in pridi in prinesi nam polno blaginjo svojo.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Bog, pomagaj nam zopet na noge; daj, da sveti obličje tvoje, in rešeni bomo.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Gospod, Bog vojnih krdél, doklej bodeš kadil proti molitvi svojega ljudstva?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Paseš jih sè solznim kruhom, in piti jim daješ sólz obilo mero.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Prepuščaš nas v prepir sosedom našim, in sovražniki naši zasmehujejo nas.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
O Bog vojnih krdel, pomagaj nam zopet na noge, in daj, da sveti obličje tvoje, rešeni bomo.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Trto si bil prestavil iz Egipta, pregnal si bil ljudstva, da bi jo zasadil.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Pospravil si bil pred njo, in storil si, da je poganjala korenine svoje, in napolnila je bila deželo.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Gore so se pokrivale sè senco njeno, in mladik njenih cedre največje.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Stezala je veje svoje noter do morja, in do reke mladike svoje.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Zakaj si podrl ograje njene, tako da jo obirajo vsi popotniki?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Izpodriva jo gozdna svinja, in žival poljska jo objeda.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
O Bog vojnih krdél, povrni se skoraj, ozri se z nebes ter glej, in obišči to trto,
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
In mladiko, katero je bila vsadila desnica tvoja, in to zavoljo sina, katerega si potrdil sebi.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Posmojena je z ognjem, odrezana; od hudovanja obličja tvojega ginejo.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Roka tvoja bodi nad možem desnice tvoje, sinom človeškim, katerega si potrdil sebi.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
In umaknili se ne bodemo od tebe; v življenji nas ohrani, da kličemo ime tvoje.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Gospod Bog vojnih krdél, pomagaj nam na noge; daj, da sveti obličje tvoje, in rešeni bomo.

< Zabura 80 >