< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
В конец, о изменшихся, свидение Асафу, псалом. Пасый Израиля вонми: наставляяй яко овча Иосифа, седяй на Херувимех, явися:
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
пред Ефремом и Вениамином и Манассием воздвигни силу Твою, и прииди во еже спасти нас.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Боже, обрати ны, и просвети лице Твое, и спасемся.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Господи Боже сил, доколе гневаешися на молитву раб Твоих?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Напитаеши нас хлебом слезным, и напоиши нас слезами в меру.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Положил еси нас в пререкание соседом нашым, и врази наши подражниша ны.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Господи Боже сил, обрати ны, и просвети лице Твое, и спасемся.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Виноград из Египта пренесл еси: изгнал еси языки, и насадил еси и:
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
путесотворил еси пред ним, и насадил еси корения его, и исполни землю.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Покры горы сень его, и ветвия его кедры Божия:
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
простре розги его до моря, и даже до рек отрасли его.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Вскую низложил еси оплот его, и оымают и вси мимоходящии путем?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Озоба и вепрь от дубравы, и уединенный дивий пояде и.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Боже сил, обратися убо, и призри с небесе и виждь, и посети виноград сей:
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
и соверши и, егоже насади десница Твоя, и на сына человеческаго, егоже укрепил еси Себе.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Пожжен огнем и раскопан: от запрещения лица Твоего погибнут.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Да будет рука Твоя на мужа десницы Твоея и на сына человеческаго, егоже укрепил еси Себе,
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
и не отступим от Тебе: оживиши ны, и имя Твое призовем.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Господи Боже сил, обрати ны, и просвети лице Твое, и спасемся.