< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
in finem pro his qui commutabuntur testimonium Asaph psalmus qui regis Israhel intende qui deducis tamquam oves Ioseph qui sedes super cherubin manifestare
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
coram Effraim et Beniamin et Manasse excita potentiam tuam et veni ut salvos facias nos
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Deus converte nos et ostende faciem tuam et salvi erimus
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Domine Deus virtutum quousque irasceris super orationem servi tui
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
cibabis nos pane lacrimarum et potum dabis nobis in lacrimis in mensura
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
posuisti nos in contradictionem vicinis nostris et inimici nostri subsannaverunt nos
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Deus virtutum converte nos et ostende faciem tuam et salvi erimus
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
vineam de Aegypto transtulisti eiecisti gentes et plantasti eam
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
dux itineris fuisti in conspectu eius et plantasti radices eius et implevit terram
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
operuit montes umbra eius et arbusta eius cedros Dei
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
extendit palmites suos usque ad mare et usque ad Flumen propagines eius
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
ut quid destruxisti maceriam eius et vindemiant eam omnes qui praetergrediuntur viam
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
exterminavit eam aper de silva et singularis ferus depastus est eam
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Deus virtutum convertere respice de caelo et vide et visita vineam istam
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
et perfice eam quam plantavit dextera tua et super filium quem confirmasti tibi
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
incensa igni et suffossa ab increpatione vultus tui peribunt
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
fiat manus tua super virum dexterae tuae et super filium hominis quem confirmasti tibi
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
et non discedimus a te vivificabis nos et nomen tuum invocabimus
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Domine Deus virtutum converte nos et ostende faciem tuam et salvi erimus

< Zabura 80 >