< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Psalmus, in finem, pro iis, qui commutabuntur, testimonium Asaph. Qui regis Israel, intende: qui deducis velut ovem Ioseph. Qui sedes super cherubim, manifestare
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
coram Ephraim, Beniamin, et Manasse. Excita potentiam tuam, et veni, ut salvos facias nos.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Deus converte nos: et ostende faciem tuam, et salvi erimus.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Domine Deus virtutum, quousque irasceris super orationem servi tui?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Cibabis nos pane lacrymarum: et potum dabis nobis in lacrymis in mensura?
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Posuisti nos in contradictionem vicinis nostris: et inimici nostri subsannaverunt nos.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Deus virtutum converte nos: et ostende faciem tuam: et salvi erimus.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Vineam de Aegypto transtulisti: eiecisti Gentes, et plantasti eam.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Dux itineris fuisti in conspectu eius: plantasti radices eius, et implevit terram.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Operuit montes umbra eius: et arbusta eius cedros Dei.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Extendit palmites suos usque ad mare: et usque ad flumen propagines eius.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Ut quid destruxisti maceriam eius: et vindemiant eam omnes, qui praetergrediuntur viam?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Exterminavit eam aper de silva: et singularis ferus depastus est eam.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Deus virtutum convertere: respice de caelo, et vide, et visita vineam istam.
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Et perfice eam, quam plantavit dextera tua: et super filium hominis, quem confirmasti tibi.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Incensa igni, et suffossa ab increpatione vultus tui peribunt.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Fiat manus tua super virum dexterae tuae: et super filium hominis, quem confirmasti tibi.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Et non discedimus a te, vivificabis nos: et nomen tuum invocabimus.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Domine Deus virtutum converte nos: et ostende faciem tuam, et salvi erimus.