< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Pour la fin, pour ceux qui seront changés, témoignage d’Asaph, psaume. Vous qui gouvernez Israël, soyez attentif: vous qui conduisez, comme une brebis, Joseph. Vous qui êtes assis sur les Chérubins, manifestez-vous
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Devant Ephraïm, Benjamin et Manassé.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Ô Dieu, convertissez-nous, et montrez votre face, et nous serons sauvés.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Seigneur, Dieu des armées, jusques à quand serez-vous irrité au sujet de la prière de votre serviteur?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Jusques à quand nous nourrirez-vous d’un pain de larmes, et nous donnerez-vous à boire des larmes dans une mesure?
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Vous nous avez posés comme un objet de contradiction à nos voisins; et nos ennemis nous ont insultés.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Dieu des armées, convertissez-nous, et montrez votre face, et nous serons sauvés.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Vous avez transporté de l’Égypte une vigne, vous avez chassé des nations, et vous l’avez plantée.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Vous avez été un guide de route devant elle: vous avez planté ses racines, et elle a rempli la terre.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Son ombre a couvert les montagnes, et ses rameaux les cèdres de Dieu.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Elle a étendu ses branches jusqu’à la mer, et ses rameaux jusqu’au fleuve.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Pourquoi donc avez-vous détruit son mur de clôture, et pourquoi la vendangent-ils, tous ceux qui passent dans le chemin?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Un sanglier de forêt l’a entièrement dévastée; et une bête sauvage l’a broutée.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Dieu des armées, revenez, regardez du haut du ciel et voyez, et visitez cette vigne.
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Faites-la prospérer, celle que votre droite à plantée, et portez vos regards sur le fils de l’homme que vous avez établi fermement pour vous.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Elle a été brûlée par le feu et déchaussée; par la réprimande de votre visage ils périront.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Que votre main repose sur l’homme de votre droite, et sur le fils de l’homme que vous avez établi fermement pour vous.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Et nous ne nous éloignerons plus de vous; vous nous rendrez la vie, et nous invoquerons votre nom.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Seigneur, Dieu des armées, convertissez-nous; et montrez votre face, et nous serons sauvés.

< Zabura 80 >