< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Psaume d'Asaph, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Sosannim-héduth. Toi qui pais Israël, prête l'oreille, toi qui mènes Joseph comme un troupeau, toi qui es assis entre les Chérubins, fais reluire ta splendeur.
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Réveille ta puissance au-devant d'Ephraïm, de Benjamin, et de Manassé; et viens pour notre délivrance.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Ô Dieu! ramène-nous, et fais reluire ta face; et nous serons délivrés.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Ô Eternel, Dieu des armées, jusques à quand seras-tu irrité contre la requête de ton peuple?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Tu les as nourris de pain de larmes, et tu les as abreuvés de pleurs à grande mesure.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Tu nous as mis pour un sujet de dispute entre nos voisins, et nos ennemis se moquent de nous entre eux.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Ô Dieu des armées ramène-nous, et fais reluire ta face; et nous serons délivrés.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Tu avais transporté une vigne hors d'Egypte; tu avais chassé les nations, et tu l'avais plantée.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Tu avais préparé une place devant elle, tu lui avais fait prendre racine, et elle avait rempli la terre.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Les montagnes étaient couvertes de son ombre, et ses rameaux étaient [comme] de hauts cèdres.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Elle avait étendu ses branches jusqu'à la mer, et ses rejetons jusqu'au fleuve.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Pourquoi as-tu rompu ses cloisons, de sorte que tous les passants en ont cueilli les raisins?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Les sangliers de la forêt l'ont détruite, et toutes sortes de bêtes sauvages l'ont broutée.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Ô Dieu des armées retourne, je te prie; regarde des cieux, vois, et visite cette vigne;
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Et le plant que ta droite avait planté, et les provins que tu avais fait devenir forts pour toi.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Elle est brûlée par feu, elle est retranchée; ils périssent dès que tu te montres pour les tancer.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Que ta main soit sur l'homme de ta droite, sur le fils de l'homme que tu t'es fortifié.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Et nous ne nous retirerons point arrière de toi. Rends-nous la vie, et nous invoquerons ton Nom.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Ô Eternel! Dieu des armées, ramène-nous, [et] fais reluire ta face; et nous serons délivrés.

< Zabura 80 >