< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Au chef des chantres. Sur les lis lyriques. D’Asaph. Psaume. Prête l’oreille, berger d’Israël, Toi qui conduis Joseph comme un troupeau! Parais dans ta splendeur, Toi qui es assis sur les chérubins!
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Devant Éphraïm, Benjamin et Manassé, réveille ta force, Et viens à notre secours!
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O Dieu, relève-nous! Fais briller ta face, et nous serons sauvés!
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Éternel, Dieu des armées! Jusques à quand t’irriteras-tu contre la prière de ton peuple?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Tu les nourris d’un pain de larmes. Tu les abreuves de larmes à pleine mesure.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Tu fais de nous un objet de discorde pour nos voisins, Et nos ennemis se raillent de nous.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Dieu des armées, relève-nous! Fais briller ta face, et nous serons sauvés!
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Tu avais arraché de l’Égypte une vigne; Tu as chassé des nations, et tu l’as plantée.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Tu as fait place devant elle: Elle a jeté des racines et rempli la terre;
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Les montagnes étaient couvertes de son ombre, Et ses rameaux étaient comme des cèdres de Dieu;
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Elle étendait ses branches jusqu’à la mer, Et ses rejetons jusqu’au fleuve.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Pourquoi as-tu rompu ses clôtures, En sorte que tous les passants la dépouillent?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Le sanglier de la forêt la ronge, Et les bêtes des champs en font leur pâture.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Dieu des armées, reviens donc! Regarde du haut des cieux, et vois! Considère cette vigne!
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Protège ce que ta droite a planté, Et le fils que tu t’es choisi!…
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Elle est brûlée par le feu, elle est coupée! Ils périssent devant ta face menaçante.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Que ta main soit sur l’homme de ta droite, Sur le fils de l’homme que tu t’es choisi!
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Et nous ne nous éloignerons plus de toi. Fais-nous revivre, et nous invoquerons ton nom.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Éternel, Dieu des armées, relève-nous! Fais briller ta face, et nous serons sauvés!