< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Au maître de chant. Sur les lis du témoignage. Psaume d’Asaph. Pasteur d’Israël, prête l’oreille, toi qui conduis Joseph comme un troupeau; toi qui trônes sur les Chérubins, parais avec splendeur.
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Devant Ephraïm, Benjamin et Manassé, réveille ta force, et viens à notre secours.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O Dieu, rétablis-nous; fais briller ta face, et nous serons sauvés.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Yahweh, Dieu des armées, jusques à quand seras-tu irrité contre la prière de ton peuple?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Tu les as nourris d’un pain de larmes, tu les as abreuvés de larmes abondantes.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Tu as fait de nous un objet de dispute pour nos voisins, et nos ennemis se raillent de nous.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Dieu des armées, rétablis-nous; fais briller sur nous ta face, et nous serons sauvés.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Tu as arraché de l’Égypte une vigne; tu as chassé les nations et tu l’as plantée.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Tu as ménagé de la place devant elle, elle a enfoncé ses racines et rempli la terre.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Son ombre couvrait les montagnes, et ses rameaux les cèdres de Dieu;
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
elle étendait ses branches jusqu’à la Mer, et ses rejetons jusqu’au Fleuve.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Pourquoi as-tu rompu ses clôtures, en sorte que tous les passants la dévastent?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Le sanglier de la forêt la dévore, et les bêtes des champs en font leur pâture.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Dieu des armées, reviens, regarde du haut du ciel et vois, considère cette vigne!
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Protège ce que ta droite a planté, et le fils que tu t’es choisi!...
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Elle est brûlée par le feu, elle est coupée; devant ta face menaçante, tout périt.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Que ta main soit sur l’homme de ta droite, sur le fils de l’homme que tu t’es choisi.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Et nous ne nous éloignerons plus de toi; rends-nous la vie, et nous invoquerons ton nom.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Yahweh, Dieu des armées, rétablis-nous; fais briller sur nous ta face, et nous serons sauvés.