< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
To the Overseer. — 'On the Lilies.' A testimony of Asaph. — A Psalm. Shepherd of Israel, give ear, Leading Joseph as a flock, Inhabiting the cherubs — shine forth,
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Before Ephraim, and Benjamin, and Manasseh, Wake up Thy might, and come for our salvation.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O God, cause us to turn back, And cause Thy face to shine, and we are saved.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Jehovah, God of Hosts, till when? Thou hast burned against the prayer of Thy people.
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Thou hast caused them to eat bread of tears, And causest them to drink With tears a third time.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Thou makest us a strife to our neighbours, And our enemies mock at it.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
God of Hosts, turn us back, And cause Thy face to shine, and we are saved.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
A vine out of Egypt Thou dost bring, Thou dost cast out nations, and plantest it.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Thou hast looked before it, and dost root it, And it filleth the land,
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Covered have been hills [with] its shadow, And its boughs [are] cedars of God.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
It sendeth forth its branches unto the sea, And unto the river its sucklings.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Why hast Thou broken down its hedges, And all passing by the way have plucked it?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
A boar out of the forest doth waste it, And a wild beast of the fields consumeth it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
God of Hosts, turn back, we beseech Thee, Look from heaven, and see, and inspect this vine,
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
And the root that Thy right hand planted, And the branch Thou madest strong for Thee,
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Burnt with fire — cut down, From the rebuke of Thy face they perish.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Let Thy hand be on the man of Thy right hand, On the son of man Thou hast strengthened for Thyself.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
And we do not go back from Thee, Thou dost revive us, and in Thy name we call.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O Jehovah, God of Hosts, turn us back, Cause Thy face to shine, and we are saved!