< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
For the chief musician, set to the Shoshannim Eduth style. A psalm of Asaph. Pay attention, Shepherd of Israel, you who lead Joseph like a flock; you who sit above the cherubim, shine on us!
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
In the sight of Ephraim and Benjamin and Manasseh, stir up your power; come and save us.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
God, restore us; make your face shine on us, and we will be saved.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Yahweh God of hosts, how long will you be angry at your people when they pray?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
You have fed them with the bread of tears and given them tears to drink in great quantities.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
You make us something for our neighbors to argue over, and our enemies laugh about us among themselves.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
God of hosts, restore us; make your face shine on us, and we will be saved.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
You brought a vine out of Egypt; you drove out nations and transplanted it.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
You cleared the land for it; it took root and filled the land.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The mountains were covered with its shade, the cedars of God by its branches.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
It sent out its branches as far as the sea and its shoots to the Euphrates River.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Why have you broken down its walls so that all who pass by along the road pluck its fruit?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
The boars out of the forest ruin it, and the beasts of the field feed on it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Turn back, God of hosts; look down from heaven and take notice and take care of this vine.
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
This is the root that your right hand planted, the shoot that you made to grow.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
It has been burned and cut down; they perish because of your rebuke.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
May your hand be on the man of your right hand, on the son of man whom you made strong for yourself.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Then we will not turn away from you; revive us, and we will call on your name.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Yahweh God of hosts, restore us; make your face shine on us, and we will be saved.

< Zabura 80 >