< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
“For the leader of the music. Upon the Shushan-Eduth. A psalm of Asaph.” Give ear, O Shepherd of Israel! Thou who leadest Joseph like a flock, Thou who sittest between the cherubs, shine forth!
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Before Ephraim and Benjamin and Manasseh, stir up thy strength, And come and save us!
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Bring us back, O God! And cause thy face to shine, that we may be saved!
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
O LORD, God of hosts! How long wilt thou be angry against the prayer of thy people?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
For thou causest them to eat the bread of tears, And givest them tears to drink, in full measure.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Thou hast made us the object of strife to our neighbors, And our enemies hold us in derision.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Bring us back, O God of hosts! And cause thy face to shine that we may be saved!
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Thou didst bring a vine out of Egypt; Thou didst expel the nations, and plant it.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Thou didst prepare a place for it; It spread its roots, and filled the land.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The mountains were covered with its shade, And its branches were like the cedars of God.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
It sent out its boughs to the sea, And its branches to the river.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Why hast thou now broken down its hedges, So that all who pass by do pluck from it?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
The boar from the wood doth waste it, And the wild beast of the forest doth devour it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
O God of hosts! return, we beseech thee, Look down from heaven, and behold, And have regard to this vine!
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Protect what thy right hand planted; The branch which thou madest strong for thyself!
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
It is burnt with fire; it is cut down; Under thy rebuke they perish.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
May thy hand be over the man of thy right hand, The man whom thou madest strong for thyself!
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
So will we no more turn back from thee: Revive us, and upon thy name alone will we call!
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Bring us back, O LORD, God of hosts! And cause thy face to shine, that we may he saved!