< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
GIVE ear, O Shepherd of Israel, thou that leadest Joseph like a flock; thou that dwellest between the cherubims, shine forth.
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Before Ephraim and Benjamin and Manasseh stir up thy strength, and come and save us.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Turn us again, O God, and cause thy face to shine; and we shall be saved.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
O Lord God of hosts, how long wilt thou be angry against the prayer of thy people?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Thou feedest them with the bread of tears; and givest them tears to drink in great measure.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Thou makest us a strife unto our neighbours: and our enemies laugh among themselves.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Turn us again, O God of hosts, and cause thy face to shine; and we shall be saved.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Thou hast brought a vine out of Egypt: thou hast cast out the heathen, and planted it.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Thou preparedst room before it, and didst cause it to take deep root, and it filled the land.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The hills were covered with the shadow of it, and the boughs thereof were like the goodly cedars.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
She sent out her boughs unto the sea, and her branches unto the river.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Why hast thou then broken down her hedges, so that all they which pass by the way do pluck her?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
The boar out of the wood doth waste it, and the wild beast of the field doth devour it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Return, we beseech thee, O God of hosts: look down from heaven, and behold, and visit this vine;
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
And the vineyard which thy right hand hath planted, and the branch that thou madest strong for thyself.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
It is burned with fire, it is cut down: they perish at the rebuke of thy countenance.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Let thy hand be upon the man of thy right hand, upon the son of man whom thou madest strong for thyself.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
So will not we go back from thee: quicken us, and we will call upon thy name.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Turn us again, O Lord God of hosts, cause thy face to shine; and we shall be saved.