< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
For the Leader; upon Shoshannim. A testimony. A Psalm of Asaph. Give ear, O Shepherd of Israel, Thou that leadest Joseph like a flock; Thou that art enthroned upon the cherubim, shine forth.
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Before Ephraim and Benjamin and Manasseh, stir up Thy might, and come to save us.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O God, restore us; and cause Thy face to shine, and we shall be saved.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
O LORD God of hosts, how long wilt Thou be angry against the prayer of Thy people?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Thou hast fed them with the bread of tears, and given them tears to drink in large measure.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Thou makest us a strife unto our neighbours; and our enemies mock as they please.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
O God of hosts, restore us; and cause Thy face to shine, and we shall be saved.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Thou didst pluck up a vine out of Egypt; Thou didst drive out the nations, and didst plant it.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Thou didst clear a place before it, and it took deep root, and filled the land.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The mountains were covered with the shadow of it, and the mighty cedars with the boughs thereof.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
She sent out her branches unto the sea, and her shoots unto the River.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Why hast Thou broken down her fences, so that all they that pass by the way do pluck her?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
The boar out of the wood doth ravage it, that which moveth in the field feedeth on it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
O God of hosts, return, we beseech Thee; look from heaven, and behold, and be mindful of this vine,
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
And of the stock which Thy right hand hath planted, and the branch that Thou madest strong for Thyself.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
It is burned with fire, it is cut down; they perish at the rebuke of Thy countenance.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Let Thy hand be upon the man of Thy right hand, upon the son of man whom Thou madest strong for Thyself.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
So shall we not turn back from Thee; quicken Thou us, and we will call upon Thy name.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O LORD God of hosts, restore us; cause Thy face to shine, and we shall be saved.