< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
For the music director. A psalm of Asaph. To the tune “Lilies of the Covenant.” Please hear us, Shepherd of Israel, you who lead the descendants of Joseph like a flock. You who sit on your throne above the cherubim, shine out
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
in the presence of Ephraim, Benjamin, and Manasseh. Gather together your power and come to save us!
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
God, please restore us! Let your face shine on us so we can be saved.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Lord God Almighty, how long will you be angry with the prayers of your people?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
You fed them with the bread of tears, and gave them a full bowl of tears to drink.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
You turn us into victims our neighbors fight over; our enemies mock us.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
God Almighty, please restore us! Let your face shine on us so we can be saved!
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
You carried us out of Egypt like a vine. You drove out the heathen nations, and then you planted the vine.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
You prepared the ground for the vine. It took root and filled the land.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The mountains were covered by its shade; its branches covered the great cedars.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
It sent its branches as far west as the Mediterranean Sea, and its shoots as far east as the Euphrates River.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
So why have you broken down the walls that protect it so that everyone who passes by can steal its fruit?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Wild pigs from the forest eat it, wild animals feed on it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
God Almighty, please return to us! Look down from heaven and see what's happening to us! Come and care for this vine
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
that you planted yourself, this son that you brought up yourself.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
We, your vine, have been chopped down and burned. May those who did this die when you glare at them.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Protect the man who stands beside you; strengthen the son you have chosen.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Then we will not turn away from you. Revive us so we can pray to you.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Lord God Almighty, please restore us! Let your face shine on us so we can be saved.

< Zabura 80 >