< Zabura 80 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
To the chief Musician. On Shoshannim-Eduth. Of Asaph. A Psalm. Give ear, O Shepherd of Israel, thou that leadest Joseph like a flock; thou that sittest [between] the cherubim, shine forth.
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Before Ephraim and Benjamin and Manasseh, stir up thy strength, and come to our deliverance.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
O God, restore us; and cause thy face to shine, and we shall be saved.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Jehovah, God of hosts, how long will thine anger smoke against the prayer of thy people?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Thou hast fed them with the bread of tears, and given them tears to drink in large measure:
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Thou hast made us a strife unto our neighbours, and our enemies mock among themselves.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Restore us, O God of hosts; and cause thy face to shine, and we shall be saved.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Thou broughtest a vine out of Egypt; thou didst cast out the nations, and plant it:
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Thou preparedst space before it, and it took deep root, and filled the land;
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
The mountains were covered with its shadow, and the branches thereof were [like] cedars of God;
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
It sent out its boughs unto the sea, and its shoots unto the river.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Why hast thou broken down its fences, so that all who pass by the way do pluck it?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
The boar out of the forest doth waste it, and the beast of the field doth feed off it.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
O God of hosts, return, we beseech thee; look down from the heavens, and behold, and visit this vine;
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
Even the stock which thy right hand hath planted, and the young plant thou madest strong for thyself.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
It is burned with fire, it is cut down; they perish at the rebuke of thy countenance.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Let thy hand be upon the man of thy right hand, upon the son of man whom thou hast made strong for thyself.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
So will we not go back from thee. Revive us, and we will call upon thy name.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Restore us, O Jehovah, God of hosts; cause thy face to shine, and we shall be saved.