< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
“A psalm of Asaph.” O God! the nations have come into thine inheritance; They have polluted thy holy temple; They have made Jerusalem a heap of ruins!
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
They have given the dead bodies of thy servants to be food for the birds of heaven, The flesh of thy holy ones to the wild beasts of the earth!
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
Their blood have they shed like water around Jerusalem, And there was none to bury them!
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We have become the reproach of our neighbors, —The scorn and derision of those around us.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
How long, O LORD! wilt thou be angry for ever? How long shall thy jealousy burn like fire?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Pour out thy wrath on the nations which acknowledge thee not. And on the kingdoms which call not upon thy name!
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
For they have devoured Jacob, And laid waste his dwelling-place.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
O remember not against us former iniquities; Let thy tender mercy speedily succor us,
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
For we are brought very low! Help us, O God of our salvation! for the honor of thy name; F or thy name's sake save us, and forgive our iniquities!
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Why should the nations say, “Where is their God?” May the revenging of the blood of thy servants, which hath been shed, Be manifested among the nations before our eyes!
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Let the cry of the prisoner come before thee! According to the greatness of thy power preserve those that are appointed to die!
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
And return sevenfold into our neighbors' bosoms The reproach with which they have reproached thee, O Lord!
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
So shall we, thy people, and the flock of thy pasture, Give thanks to thee for ever. And show forth thy praise to all generations.

< Zabura 79 >