< Zabura 79 >
1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
O God, the heathen are come into your inheritance; your holy temple have they defiled; they have laid Jerusalem on heaps.
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
The dead bodies of your servants have they given to be meat to the fowls of the heaven, the flesh of your saints to the beasts of the earth.
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
Their blood have they shed like water round about Jerusalem; and there was none to bury them.
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
We are become a reproach to our neighbors, a scorn and derision to them that are round about us.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
How long, LORD? will you be angry for ever? shall your jealousy burn like fire?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Pour out your wrath on the heathen that have not known you, and on the kingdoms that have not called on your name.
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
For they have devoured Jacob, and laid waste his dwelling place.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
O remember not against us former iniquities: let your tender mercies speedily prevent us: for we are brought very low.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Help us, O God of our salvation, for the glory of your name: and deliver us, and purge away our sins, for your name’s sake.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Why should the heathen say, Where is their God? let him be known among the heathen in our sight by the revenging of the blood of your servants which is shed.
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Let the sighing of the prisoner come before you; according to the greatness of your power preserve you those that are appointed to die;
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
And render to our neighbors sevenfold into their bosom their reproach, with which they have reproached you, O Lord.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
So we your people and sheep of your pasture will give you thanks for ever: we will show forth your praise to all generations.