< Zabura 79 >

1 Zabura ta Asaf. Ya Allah, al’ummai sun mamaye gādonka; sun ƙazantar da haikalinka mai tsarki, sun bar Urushalima kufai.
Асафов псалом. Боже, народите дойдоха в наследството Ти, Оскверниха светия Твой храм, Обърнаха Ерусалим на развалини,
2 Sun ba da gawawwakin bayinka kamar abinci ga tsuntsayen sararin sama, nama jikin tsarkakanka ga namun jejin duniya.
Мъртвите тела на слугите Ти дадоха за ястие на небесните птици, Месата на светиите Ти на земните зверове,
3 Sun zubar da jini kamar ruwa ko’ina a Urushalima, kuma babu wani da zai binne matattu.
Проляха кръвта им като вода около Ерусалим; И нямаше кой да ги погребва.
4 Mun zama abin reni ga maƙwabta, abin ba’a da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Станахме за укор пред съседите си, Присмех и поругание пред околните си.
5 Har yaushe, ya Ubangiji za ka yi ta fushi? Har abada ne? Har yaushe kishinka zai yi ta ƙuna kamar wuta?
До кога, Господи? Ще се гневиш ли винаги? Ще гори ли като огън ревността Ти?
6 Ka zuba fushinka a kan al’umman da ba su yarda da kai ba, a kan mulkokin da ba sa kira bisa sunanka;
Излей гнева Си на народите, които не Те познават, И на царствата, които не призовават името Ти;
7 gama sun cinye Yaƙub suka lalatar da ƙasar zamansa.
Защото изпоядоха Якова, И пасбищата му запустяха.
8 Kada ka riƙe zunubai kakanni a kanmu; bari jinƙanka yă zo da sauri yă sadu da mu, gama mun fid da zuciya sarai.
Не спомняй против нас беззаконията на прадедите ни Дано ни предварят скоро Твоите благи милости. Защото станахме много окаяни.
9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, saboda ɗaukakar sunanka; ka cece mu ka kuma gafarta mana zunubanmu saboda sunanka.
Помогни ни, Боже Спасителю наш, заради славата на Твоето име; Избави ни и очисти греховете ни, заради името Си.
10 Don me al’ummai za su ce, “Ina Allahnsu yake?” A idanunmu, ka sanar wa al’ummai cewa kana ɗaukan fansar jinin bayinka da aka zubar.
Защо да рекат народите: Где е техният Бог? Нека се знае, пред очите ни, между народите Възмездието за пролятата кръв на слугите Ти.
11 Bari nishe-nishen’yan kurkuku su zo gabanka; ta wurin ƙarfin hannunka ka kiyaye waɗanda aka yanke wa hukuncin mutuwa.
Нека дойде пред Тебе въздишането на затворниците; Според великата Твоя сила опази осъдените на смърт;
12 Ka sāka a cinyoyin maƙwabtanmu sau bakwai zage-zagen da suka yi ta yi maka, ya Ubangiji.
И възвърни седмократно в пазухата на съседите ни Укора, с който укориха Тебе, Господи.
13 Sa’an nan mu mutanenka, tumakin makiyayarka, za mu yabe ka har abada; daga tsara zuwa tsara za mu yi ta ba da labarin yabonka.
Така ние, Твоите люде и овцете на пасбището Ти, Ще те славословим до века, Из род в род ще разгласяваме Твоята хвала.

< Zabura 79 >