< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Masquil de Asaph. ESCUCHA, pueblo mío, mi ley: inclinad vuestro oído á las palabras de mi boca.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Abriré mi boca en parábola; hablaré cosas reservadas de antiguo:
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Las cuales hemos oído y entendido; que nuestros padres nos [las] contaron.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
No las encubriremos á sus hijos, contando á la generación venidera las alabanzas de Jehová, y su fortaleza, y sus maravillas que hizo.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
El estableció testimonio en Jacob, y pusó ley en Israel; la cual mandó á nuestros padres que la notificasen á sus hijos;
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
Para que [lo] sepa la generación venidera, y los hijos que nacerán; y [los que] se levantarán, [lo] cuenten á sus hijos;
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
A fin de que pongan en Dios su confianza, y no se olviden de las obras de Dios, y guarden sus mandamientos:
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
Y no sean como sus padres, generación contumaz y rebelde; generación que no apercibió su corazón, ni fué fiel para con Dios su espíritu.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Los hijos de Ephraim armados, flecheros, volvieron [las espaldas] el día de la batalla.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
No guardaron el pacto de Dios, ni quisieron andar en su ley:
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Antes se olvidaron de sus obras, y de sus maravillas que les había mostrado.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Delante de sus padres hizo maravillas en la tierra de Egipto, en el campo de Zoán.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Rompió la mar, é hízolos pasar; é hizo estar las aguas como en un montón.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Y llevólos de día con nube, y toda la noche con resplandor de fuego.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Hendió las peñas en el desierto: y dióles á beber como de grandes abismos;
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Pues sacó de la peña corrientes, é hizo descender aguas como ríos.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Empero aun tornaron á pecar contra él, enojando en la soledad al Altísimo.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Pues tentaron á Dios en su corazón, pidiendo comida á su gusto.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Y hablaron contra Dios, diciendo: ¿Podrá poner mesa en el desierto?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
He aquí ha herido la peña, y corrieron aguas, y arroyos salieron ondeando: ¿podrá también dar pan? ¿aparejará carne á su pueblo?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Por tanto oyó Jehová, é indignóse: y encendióse el fuego contra Jacob, y el furor subió también contra Israel;
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Por cuanto no habían creído á Dios, ni habían confiado en su salud:
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
A pesar de que mandó á las nubes de arriba, y abrió las puertas de los cielos,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
E hizo llover sobre ellos maná para comer, y dióles trigo de los cielos.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Pan de nobles comió el hombre: envióles comida á hartura.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Movió el solano en el cielo, y trajo con su fortaleza el austro.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
E hizo llover sobre ellos carne como polvo, y aves de alas como arena de la mar.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
E hízolas caer en medio de su campo, alrededor de sus tiendas.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Y comieron, y hartáronse mucho: cumplióles pues su deseo.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
No habían quitado de sí su deseo, aun estaba su vianda en su boca,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
Cuando vino sobre ellos el furor de Dios, y mató los más robustos de ellos, y derribó los escogidos de Israel.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Con todo esto pecaron aún, y no dieron crédito á sus maravillas.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Consumió por tanto en nada sus días, y sus años en la tribulación.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Si los mataba, entonces buscaban á Dios; entonces se volvían solícitos en busca suya.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Y acordábanse que Dios era su refugio, y el Dios Alto su redentor.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Mas le lisonjeaban con su boca, y con su lengua le mentían:
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Pues sus corazones no eran rectos con él, ni estuvieron firmes en su pacto.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Empero él misericordioso, perdonaba la maldad, y no [los] destruía: y abundó para apartar su ira, y no despertó todo su enojo.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Y acordóse que eran carne; soplo que va y no vuelve.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
¡Cuántas veces lo ensañaron en el desierto, lo enojaron en la soledad!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Y volvían, y tentaban á Dios, y ponían límite al Santo de Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
No se acordaron de su mano, del día que los redimió de angustia;
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Cuando puso en Egipto sus señales, y sus maravillas en el campo de Zoán;
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Y volvió sus ríos en sangre, y sus corrientes, porque no bebiesen.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Envió entre ellos una mistura de moscas que los comían, y ranas que los destruyeron.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Dió también al pulgón sus frutos, y sus trabajos á la langosta.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Sus viñas destruyó con granizo, y sus higuerales con piedra;
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Y entregó al pedrisco sus bestias, y al fuego sus ganados.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Envió sobre ellos el furor de su saña, ira y enojo y angustia, con misión de malos ángeles.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Dispuso el camino á su furor; no eximió la vida de ellos de la muerte, sino que entregó su vida á la mortandad.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
E hirió á todo primogénito en Egipto, las primicias de las fuerzas en las tiendas de Châm.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Empero hizo salir á su pueblo como ovejas, y llevólos por el desierto, como un rebaño.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Y guiólos con seguridad, que no tuvieron miedo; y la mar cubrió á sus enemigos.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Metiólos después en los términos de su santuario, en este monte que ganó su mano derecha.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Y echó las gentes de delante de ellos, y repartióles una herencia con cuerdas; é hizo habitar en sus moradas á las tribus de Israel.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Mas tentaron y enojaron al Dios Altísimo, y no guardaron sus testimonios;
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Sino que se volvieron, y se rebelaron como sus padres: volviéronse como arco engañoso.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Y enojáronlo con sus altos, y provocáronlo á celo con sus esculturas.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Oyólo Dios, y enojóse, y en gran manera aborreció á Israel.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Dejó por tanto el tabernáculo de Silo, la tienda [en que] habitó entre los hombres;
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Y dió en cautividad su fortaleza, y su gloria en mano del enemigo.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Entregó también su pueblo á cuchillo, y airóse contra su heredad.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
El fuego devoró sus mancebos, y sus vírgenes no fueron loadas en cantos nupciales.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Sus sacerdotes cayeron á cuchillo, y sus viudas no lamentaron.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Entonces despertó el Señor á la manera del que ha dormido, como un valiente que grita excitado del vino:
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
E hirió á sus enemigos en las partes posteriores: dióles perpetua afrenta.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Y desechó el tabernáculo de José, y no escogió la tribu de Ephraim;
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Sino que escogió la tribu de Judá, el monte de Sión, al cual amó.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Y edificó su santuario á manera de eminencia, como la tierra que cimentó para siempre.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Y eligió á David su siervo, y tomólo de las majadas de las ovejas:
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
De tras las paridas lo trajo, para que apacentase á Jacob su pueblo, y á Israel su heredad.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Y apacentólos con entereza de su corazón; y pastoreólos con la pericia de sus manos.

< Zabura 78 >