< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Escucha, pueblo mío, mi instrucción. Inclina tus oídos a las palabras de mi boca.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Abriré mi boca en proverbio. Declararé dichos de antaño de difícil comprensión,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Los cuales oímos y conocimos. Nos los relataron nuestros antepasados.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
No los encubriremos a sus hijos. Contaremos a la generación venidera las alabanzas de Yavé, Y su poder y las maravillosas obras que hizo.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Él estableció testimonio en Jacob, Y estableció Ley en Israel, La cual mandó a nuestros antepasados Que la enseñaran a sus hijos,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
A fin de que la generación venidera [la] supiera, Los hijos que iban a nacer, Con el fin de que se levantaran y la dijeran a sus hijos,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
Para que en ʼElohim depositen su confianza, Y no olviden las obras de ʼEL, Sino que guarden sus Mandamientos,
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
Y no sean como sus antepasados, Generación terca y rebelde, Generación que no preparó su corazón, Y su espíritu no fue fiel a ʼEL.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Los hijos de Efraín, arqueros equipados, Dieron la espalda en el día de la batalla.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
No guardaron el Pacto de ʼElohim Y rehusaron andar en su Ley.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Olvidaron sus obras. Él hizo maravillas ante sus antepasados en la tierra de Egipto.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Delante de sus antepasados realizó maravillas en la tierra de Egipto. En el campo de Zoán
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Dividió el mar y los pasó. Detuvo las aguas como en una pila.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
De día los guiaba con nube, Con resplandor de fuego toda la noche.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Hendió las peñas del desierto Y les dio a beber raudales sin medida.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Sacó arroyos de la peña Y las aguas corrieron como ríos.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Pero ellos aún continuaron pecando contra Él. Se rebelaron contra ʼElyón en el desierto
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Y en sus corazones tentaron a ʼEL. Pidieron comida según su deseo.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Hablaron contra ʼElohim: ¿Puede ʼEL preparar una mesa en el desierto?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Sí, Él golpeó la roca Y brotaron aguas y se desbordaron torrentes. ¿Puede Él dar también pan? ¿Proveerá carne para su pueblo?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Por tanto, oyó Yavé y se indignó. Un fuego se encendió contra Jacob, Y una ira subió contra Israel,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Por cuanto no creyeron en ʼElohim, Ni confiaron en su salvación.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Sin embargo, mandó a las nubes desde arriba, Y abrió las puertas del cielo.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Hizo llover sobre ellos maná para comer Y les dio alimento del cielo.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Pan de ángeles comió el hombre. Les envió comida en abundancia.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Sopló en el cielo el viento del este Y con su poder atrajo el viento del sur.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Esparció sobre ellos carne como polvo, Criaturas aladas como la arena de los mares.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Las soltó en medio del campamento alrededor de sus tiendas.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Comieron y se hartaron, Y les cumplió su deseo.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Antes que ellos saciaran su apetito, Cuando la comida estaba en sus bocas,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
Surgió contra ellos la ira divina Que mató a algunos de los fornidos de ellos Y sometió a los jóvenes escogidos de Israel.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
A pesar de eso, siguieron en pecado Y no dieron crédito a sus maravillas.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Por tanto consumió sus días en vanidad, Y sus años en temor.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Cuando los hería de muerte, Lo buscaban. Se arrepentían y con diligencia lo buscaban.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Se acordaban que ʼElohim era su Roca, Y ʼEL, ʼElyón, su Redentor.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Lo lisonjeaban con su boca Y le mentían con su lengua.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Pues sus corazones no eran firmes hacia Él, Ni eran fieles a su Pacto.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Pero Él por misericordia perdonó su iniquidad Y no los destruyó. Con frecuencia contuvo su ira Y no despertó todo su enojo.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Recordó que no eran sino carne, Un soplo que pasa y no regresa.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
¡Cuán a menudo se rebelaron contra Él en el desierto Y lo contristaron en terreno no habitado!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Vez tras vez tentaron a ʼEL. Irritaron al Santo de Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
No se acordaron de su poder, Del día cuando los redimió del adversario:
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Cuando realizó en Egipto sus señales, Y sus maravillas en la tierra de Zoán.
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Cuando convirtió sus ríos en sangre, Y ellos no pudieron beber de sus manantiales.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Cuando envió entre ellos enjambres de moscas que los devoraban Y ranas que los destruían.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Cuando entregó a los saltamontes sus cosechas Y el fruto de su trabajo a la langosta.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Él destruyó sus viñas con granizo Y sus sicómoros con escarcha.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Él entregó al granizo sus vacadas Y a los rayos sus ganados.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Envió sobre ellos su ardiente ira, Enojo, indignación y angustia, Una banda de mensajeros destructores.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Él dispuso un camino para su ira Y no libró sus vidas de la muerte. Entregó sus vidas a la pestilencia
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
E hirió a todos los primogénitos de Egipto, Las primicias de su virilidad en las tiendas de Cam.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Pero dirigió a su pueblo como ovejas, Y como rebaño los guió por el desierto.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Los condujo con seguridad para que no temieran, Pero el mar cubrió a sus enemigos.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Los llevó hasta la frontera de su Tierra Santa, Al país montañoso que adquirió su mano derecha.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Echó a las naciones de delante de ellos. Con medida [les] repartió las tierras de ellos en heredad, E hizo que las tribus de Israel vivieran en sus tiendas.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Pero ellos tentaron y provocaron a ʼElyón ʼElohim Y no guardaron sus Testimonios.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Regresaron y actuaron deslealmente como sus antepasados. Tal como sus antepasados, fueron desleales. Se desviaron como arco torcido.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Lo provocaron con sus lugares altos Y despertaron su celo con sus imágenes de talla.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Cuando ʼElohim oyó, se indignó Y aborreció a Israel en gran manera.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Por lo cual abandonó el Tabernáculo de Silo, El Tabernáculo que estableció entre los hombres.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Entregó su poder a la cautividad Y su resplandor en mano del adversario.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Entregó también su pueblo a la espada Y se indignó contra su heredad.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
El fuego devoró a sus jóvenes, Y sus doncellas no tuvieron cantos nupciales.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Sus sacerdotes cayeron a espada, Y sus viudas no hicieron lamentación.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Pero entonces, como el que duerme, Como un valiente que se recupera del vino Despertó ʼAdonay
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
E hirió a sus adversarios por detrás. Puso sobre ellos afrenta perpetua.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Desechó la tienda de José Y no eligió a la tribu de Efraín,
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Sino escogió a la tribu de Judá Y la Montaña de Sion, que Él amó.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Construyó en las alturas su Santuario Como la tierra que fundó para siempre.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
También escogió a David, su esclavo, Y lo tomó de los rebaños.
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Lo trajo de detrás de las ovejas que tenían crías Para que apacentara a Jacob su pueblo Y a Israel su heredad.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Los pastoreó según la integridad de su corazón, Y los guió con la destreza de sus manos.