< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Instrução de Asafe: Povo meu, escuta minha doutrina; inclinai vossos ouvidos às palavras de minha boca.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Abrirei minha boca em parábolas; falarei mistérios dos tempos antigos,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Os quais ouvimos e conhecemos, e nossos pais nos contaram.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Nós não [os] encobriremos a seus filhos, contaremos à próxima geração sobre os louvores do SENHOR, o seu poder, e suas maravilhas que ele fez.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Porque ele firmou um testemunho em Jacó, e pôs a Lei em Israel, a qual ele instruiu aos nossos pais, para que eles ensinassem a seus filhos;
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
Para que a geração seguinte [dela] soubesse; [e] os filhos que nascessem contassem a seus filhos;
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
E [assim] pusessem sua esperança em Deus; e não se esquecessem dos feitos de Deus, mas sim, que guardassem os mandamentos dele;
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
E não fossem como seus pais, [que foram] uma geração teimosa e rebelde; geração que não firmou seu coração, e cujo espírito não foi fiel a Deus.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Os filhos de Efraim, mesmo tendo arcos e flechas, viraram-se para trás no dia da batalha;
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Não guardaram o pacto de Deus, e recusaram a andar conforme sua Lei.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
E se esqueceram de seus feitos, e de suas maravilhas que ele tinha lhes feito ver.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Ele fez maravilhas perante seus pais na terra do Egito, [no] campo de Zoã.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Ele dividiu o mar, e os fez passarem por ele; ele fez as águas ficarem paradas como [se estivessem] amontoadas.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
E ele os guiou com uma nuvem durante o dia, e por toda a noite com uma luz de fogo.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Ele partiu as rochas no deserto, e [lhes] deu de beber como que de abismos profundos.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Porque ele tirou correntes da rocha, e fez as águas descerem como rios.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
E [ainda] prosseguiram em pecar contra ele, irritando ao Altíssimo no deserto.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
E tentaram a Deus nos seus corações, pedindo comida para o desejo de suas almas.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
E falaram contra Deus, e disseram: Poderia Deus preparar uma mesa de comida no deserto?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Eis que ele feriu a rocha, e águas correram [dela] e ribeiros fluíram em abundância; será que ele também poderia [nos] dar pão, ou preparar carne a seu povo?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Por isso o SENHOR [os] ouviu, e se irritou; e fogo se acendeu contra Jacó, e furor também subiu contra Israel;
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Porque eles não creram em Deus, nem confiaram na salvação que dele vem;
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Mesmo assim, ele deu ordens às altas nuvens, e abriu as portas dos céus;
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
E choveu sobre eles o maná, para comerem; e lhes deu trigo dos céus.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Cada homem [daquele povo] comeu o pão dos anjos; ele lhes mandou comida para se fartarem.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Ele fez soprar o vento do oriente nos céus, e trouxe o [vento] do sul com seu poder.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Ele fez chover sobre eles carne como a poeira da terra; e aves de asas como a areia do mar;
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
E [as] fez cair no meio de seu acampamento, ao redor de suas tendas.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Então comeram, e fartaram-se abundantemente; e satisfez o desejo deles.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Porem, estando eles [ainda] não satisfeitos, enquanto a comida ainda estava em suas bocas,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
a ira de Deus subiu contra eles; matou os mais robustos deles e abateu os jovens de Israel.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Com tudo isto ainda pecaram, e não creram nas maravilhas que ele fez.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Por isso gastaram seus dias em futilidades, e seus anos em terrores.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Quando ele matava [alguns dentre] eles, então buscavam por ele, e se convertiam, e buscavam a Deus de madrugada.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
E se lembravam de que Deus era sua rocha, e que o Deus Altíssimo [era] o seu libertador.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Porém falavam bem dele da boca para fora, e mentiam com suas línguas.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Porque o coração deles não era comprometido para com ele, e não foram fiéis ao pacto dele.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Porém ele, sendo misericordioso, perdoava a maldade deles, e não os destruía; e muitas vezes desviou de mostrar sua ira, e não despertou todo o seu furor;
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
[Porque] se lembrou de que eles eram carne, e [como] o vento, que vai, e não volta mais.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Quantas vezes o provocaram no deserto, e o maltrataram na terra desabitada!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Pois voltavam a tentar a Deus, e perturbavam ao Santo de Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Não se lembraram de sua mão, [nem] do dia em que os livrou do adversário.
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Como quando ele fez seus sinais no Egito, e seus atos maravilhosos no campo de Zoã.
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
E transformou seus rios e suas correntes em sangue, para que não bebessem.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Enviou entre eles variedades de moscas, que os consumiu; e rãs, que os destruíram.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
E deu suas colheitas ao pulgão, e o trabalho deles ao gafanhoto.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Com saraiva destruiu suas vinhas, e suas figueiras-bravas com granizo.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
E entregou seu gado à saraiva; e seus animais a brasas ardentes.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Mandou entre eles o ardor de sua ira: fúria, irritação e angústia, enviando mensageiros do mal.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Ele preparou o caminho de sua ira; não poupou suas almas da morte, e entregou seus animais à peste.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
E feriu [mortalmente] a todo primogênito no Egito; as primícias nas forças nas tendas de Cam.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
E levou a seu povo como a ovelhas; e os guiou pelo deserto como a um rebanho.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Ele os conduziu em segurança, e não temeram. O mar encobriu seus inimigos.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
E os trouxe até os limites de sua [terra] santa, até este monte, que sua mão direita adquiriu.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
E expulsou as nações de diante deles, e fez com que eles repartissem as linhas de sua herança, e fez as tribos de Israel habitarem em suas tendas.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Porém eles tentaram e provocaram ao Deus Altíssimo; e não guardaram os testemunhos dele.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
E voltaram a ser [tão] infiéis como os seus pais; desviaram-se como um arco enganoso.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
E provocaram a ira dele com seus altares pagãos, e com suas imagens de escultura moveram-no de ciúmes.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Deus ouviu [isto], e se indignou; e rejeitou gravemente a Israel.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Por isso ele abandonou o tabernáculo em Siló, a tenda que ele havia estabelecido como habitação entre as pessoas.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
E entregou o [símbolo] de seu poder em cativeiro, e sua glória na mão do adversário.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
E entregou seu povo à espada, e enfureceu-se contra sua herança.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
O fogo consumiu a seus rapazes, e suas virgens não tiveram músicas de casamento.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Seus sacerdotes caíram à espada, e suas viúvas não lamentaram.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Então o Senhor despertou como que do sono, como um homem valente que se exalta com o vinho.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
E feriu a seus adversários, para que recuassem, [e] lhes pôs como humilhação perpétua.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Porém ele rejeitou a tenda de José, e não escolheu a tribo de Efraim.
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Mas escolheu a tribo de Judá, o monte de Sião, a quem ele amava.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
E edificou seu santuário como alturas; como a terra, a qual ele fundou para sempre.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
E ele escolheu a seu servo Davi; e o tomou dos apriscos de ovelhas.
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Ele o tirou de cuidar das ovelhas geradoras de filhotes, para que ele apascentasse ao seu povo Jacó; e à sua herança Israel.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
E ele os apascentou com um coração sincero, e os guiou com as habilidades de suas mãos.