< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Lalelani, bantu bami, umthetho wami, libeke indlebe yenu emazwini omlomo wami.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Ngizavula umlomo wami ngomfanekiso, ngikhuphe izimfihlakalo zendulo,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
esizizwileyo lesizaziyo, obaba abasitshela zona.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Kasiyikuzifihlela abantwana babo, kusizukulwana esilandelayo, silandisa izindumiso zeNkosi, lamandla ayo, lezimangaliso ezenzileyo.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Ngoba wamisa ubufakazi koJakobe, wabeka umlayo koIsrayeli, awulaya obaba, ukuze bawazise abantwana babo,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
ukuze isizukulwana esilandelayo sazi, abantwana abazazalwa, basukume batshele abantwana babo,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
ukuze babeke ithemba labo kuNkulunkulu, bangayikhohlwa imisebenzi kaNkulunkulu, kodwa bagcine imithetho yakhe;
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
njalo bangabi njengaboyise, isizukulwana esilenkani lesivukelayo, isizukulwana esingaqondisanga inhliziyo yaso, lesimoya waso ungathembekanga kuNkulunkulu.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Abantwana bakoEfrayimi, behlomile betshoka ngamadandili, babuyela emuva mhla wempi.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Kabasilondolozanga isivumelwano sikaNkulunkulu, bala ukuhamba emlayweni wakhe.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Bakhohlwa izenzo zakhe lezimangaliso zakhe ayebatshengisa zona.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Phambi kwaboyise wenza isimangaliso elizweni leGibhithe, egangeni leZowani.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Waqhekeza ulwandle, wabachaphisa, wenza amanzi ema njengenqumbi.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Wabakhokhela ngeyezi emini, lebusuku bonke ngokukhanya komlilo.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Waqhekeza amadwala enkangala, wabanathisa kungathi kuvela ezinzikini ezinkulu.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Waseveza izifula edwaleni, wenza amanzi ehla njengemifula.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Kodwa baphinda futhi ukona kuye, ngokumvukela oPhezukonke enkangala.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Bamlinga uNkulunkulu enhliziyweni yabo ngokucela ukudla kwenkanuko yabo.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Basebekhuluma bemelene loNkulunkulu bathi: UNkulunkulu angalungisa itafula enkangala yini?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Khangela, watshaya idwala, kwampompoza amanzi, lezifula zagabha; anganika lesinkwa yini? angalungisela abantu bakhe inyama na?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Ngakho iNkosi yezwa yathukuthela; umlilo wasubaselwa uJakobe, njalo lolaka lwavukela uIsrayeli,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
ngoba kabakholwanga kuNkulunkulu, kabathembanga esindisweni lwakhe.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Lanxa walaya amayezi ngaphezulu, wavula iminyango yamazulu,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
wabanisela imana ukuthi badle, wabapha amabele amazulu.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Umuntu wadla isinkwa sabalamandla; wabathumela ukudla ukuze basuthe.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Wenza umoya wempumalanga wavunguza emazulwini; langamandla akhe waqhuba umoya weningizimu.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Wasenisela phezu kwabo inyama njengothuli, lenyoni ezilempiko njengetshebetshebe lolwandle;
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
wazenza zawela phakathi kwenkamba yabo, zagombolozela indawo zabo zokuhlala.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Ngakho badla basutha kakhulu, ngoba wabalethela isiloyiso sabo.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Kabehlukananga lenkanuko yabo; ukudla kusesemlonyeni wabo,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
ulaka lukaNkulunkulu lwaselubavukela, wabulala kwabakhulupheleyo babo, watshaya abakhethiweyo bakoIsrayeli.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Kulokhu konke bajinga besona, njalo kabakholwanga ngenxa yezimangaliso zakhe.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Ngakho waziqeda izinsuku zabo ngeze, leminyaka yabo ovalweni.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Lapho ebabulala, bamdinga, baphenduka, bamdingisisa uNkulunkulu.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Bakhumbula ukuthi uNkulunkulu ulidwala labo, loNkulunkulu oPhezukonke ungumhlengi wabo.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Kodwa bamyenga ngomlomo wabo, baqamba amanga kuye ngolimi lwabo.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Ngoba inhliziyo yabo yayingaqondanga kuye, njalo bengathembekanga esivumelwaneni sakhe.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Kodwa yena elesihawu wathethelela ububi babo, kababhubhisanga; yebo, kanengi walunqanda ulaka lwakhe, kakuvusanga konke ukuthukuthela kwakhe.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Ngoba wakhumbula ukuthi bayinyama, umoya odlulayo, ongabuyiyo.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Kanengi kangakanani bemvukela ehlane, bemdabukisa enkangala.
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Yebo baphenduka bamlinga uNkulunkulu, bamdabukisa oNgcwele kaIsrayeli.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Kabasikhumbulanga isandla sakhe, usuku abahlenga ngalo esitheni.
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Ukuthi wamisa njani izibonakaliso zakhe eGibhithe, lezimangaliso zakhe emmangweni weZowani,
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
lokuthi waphendula imifula yabo yaba ligazi, lezifula zabo, ukuze banganathi.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Wathumela phakathi kwabo umtshitshi wezibawu, ezabadlayo, lamaxoxo ababhubhisayo.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Wasenika imihogoyi isivuno sabo, lomsebenzi wabo isikhonyane.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Wabulala ivini labo ngesiqhotho, lemikhiwa yabo yesikhamore ngongqwaqwane.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Wasenikela izifuyo zabo esiqhothweni, lemihlambi yabo kuyo imibane.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Waphosela phezu kwabo ukuvutha kolaka lwakhe, ukuthukuthela, lokucunuka, lokuhlupheka, ngokuthuma izithunywa zobubi.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Walungisela ulaka lwakhe indlela, kanqandanga umphefumulo wabo ekufeni, kodwa wanikela impilo yabo kumatshayabhuqe wesifo.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Wasetshaya wonke amazibulo eGibhithe, okokuqala kwamandla emathenteni kaHamu.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Wasebakhupha abantu bakhe njengezimvu, wabakhokhela enkangala njengomhlambi.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Wasebakhokhela bephephile ukuze bangesabi; kodwa ulwandle lwasibekela izitha zabo.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Wasebafikisa emkhawulweni wendawo yakhe engcwele, le intaba, isandla sakhe sokunene esayizuzayo.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Wasebaxotsha abezizwe phambi kwabo; wababela ilifa ngomzila, wahlalisa izizwe zakoIsrayeli emathenteni azo.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Kanti bamlinga, bamvukela uNkulunkulu oPhezukonke, kabazigcinanga izifakazelo zakhe.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Kodwa babuyela emuva, benza ngokungathembeki njengaboyise, baphanjulwa njengedandili elikhohlisayo.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Ngoba bamthukuthelisa ngezindawo zabo eziphakemeyo, bavusa umona wakhe ngezithombe zabo ezibaziweyo.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
UNkulunkulu esizwa wathukuthela, wamenyanya kakhulu uIsrayeli.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Ngakho walitshiya ithabhanekele leShilo, ithente alimisa phakathi kwabantu.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Wasenikela amandla akhe ekuthunjweni, lenkazimulo yakhe esandleni sesitha.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Wasenikela abantu bakhe enkembeni, waselithukuthelela ilifa lakhe.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Umlilo waqeda amajaha abo, lezintombi zabo kazihlatshelelwanga.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Abapristi babo bawa ngenkemba, labafelokazi babo kabalilanga.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Khona iNkosi yavuka njengobelele, njengeqhawe eliklabalala ngenxa yewayini.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Yazitshaya izitha zayo emuva, yazithela ihlazo phakade.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Yasilahla ithente likaJosefa, kayikhethanga isizwe sakoEfrayimi.
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Kodwa yakhetha isizwe sakoJuda, intaba yeZiyoni eyithandayo.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Yayakha indlu yayo engcwele njengezingqonga, njengomhlaba ewusekeleyo kuze kube nininini.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Yasikhetha uDavida inceku yayo, yamthatha ezibayeni zezimvu;
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
ekulandeleni izimvukazi ezenyisayo, yamletha ukwelusa uJakobe abantu bayo, loIsrayeli ilifa layo.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Njalo wabelusa njengobuqotho benhliziyo yakhe, wabakhokhela ngobugabazi bezandla zakhe.

< Zabura 78 >