< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Intellectus Asaph. Attendite popule meus legem meam: inclinate aurem vestram in verba oris mei.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Aperiam in parabolis os meum: loquar propositiones ab initio.
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Quanta audivimus et cognovimus ea: et patres nostri narraverunt nobis.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Non sunt occultata a filiis eorum, in generatione altera. Narrantes laudes Domini, et virtutes eius, et mirabilia eius quæ fecit.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Et suscitavit testimonium in Iacob: et legem posuit in Israel. Quanta mandavit patribus nostris nota facere ea filiis suis:
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
ut cognoscat generatio altera. Filii qui nascentur, et exurgent, et narrabunt filiis suis,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
Ut ponant in Deo spem suam, et non obliviscantur operum Dei: et mandata eius exquirant.
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
Ne fiant sicut patres eorum: generatio prava et exasperans. Generatio, quæ non direxit cor suum: et non est creditus cum Deo spiritus eius.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Filii Ephrem intendentes et mittentes arcum: conversi sunt in die belli.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Non custodierunt testamentum Dei, et in lege eius noluerunt ambulare.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Et obliti sunt benefactorum eius, et mirabilium eius quæ ostendit eis.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Coram patribus eorum fecit mirabilia in terra Ægypti, in campo Taneos.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Interrupit mare, et perduxit eos: et statuit aquas quasi in utre.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Et deduxit eos in nube diei: et tota nocte in illuminatione ignis.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Interrupit petram in eremo: et adaquavit eos velut in abysso multa.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Et eduxit aquam de petra: et deduxit tamquam flumina aquas.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Et apposuerunt adhuc peccare ei: in iram excitaverunt Excelsum in inaquoso.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Et tentaverunt Deum in cordibus suis: ut peterent escas animabus suis.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Et male locuti sunt de Deo: dixerunt: Numquid poterit Deus parare mensam in deserto?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Quoniam percussit petram, et fluxerunt aquæ, et torrentes inundaverunt. Numquid et panem poterit dare, aut parare mensam populo suo?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Ideo audivit Dominus, et distulit: et ignis accensus est in Iacob, et ira ascendit in Israel:
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Quia non crediderunt in Deo, nec speraverunt in salutari eius:
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Et mandavit nubibus desuper, et ianuas cæli aperuit.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Et pluit illis manna ad manducandum, et panem cæli dedit eis.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Panem angelorum manducavit homo: cibaria misit eis in abundantia.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Transtulit Austrum de cælo: et induxit in virtute sua Africum.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Et pluit super eos sicut pulverem carnes, et sicut arenam maris volatilia pennata.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Et ceciderunt in medio castrorum eorum: circa tabernacula eorum.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Et manducaverunt et saturati sunt nimis, et desiderium eorum attulit eis:
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
non sunt fraudati a desiderio suo. Adhuc escæ eorum erant in ore ipsorum,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
et ira Dei ascendit super eos. Et occidit pingues eorum, et electos Israel impedivit.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
In omnibus his peccaverunt adhuc: et non crediderunt in mirabilibus eius.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Et defecerunt in vanitate dies eorum: et anni eorum cum festinatione.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Cum occideret eos, quærebant eum: et revertebantur, et diluculo veniebant ad eum.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Et rememorati sunt quia Deus adiutor est eorum: et Deus excelsus redemptor eorum est.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Et dilexerunt eum in ore suo, et lingua sua mentiti sunt ei:
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Cor autem eorum non erat rectum cum eo: nec fideles habiti sunt in testamento eius.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Ipse autem est misericors, et propitius fiet peccatis eorum: et non disperdet eos. Et abundavit ut averteret iram suam: et non accendit omnem iram suam:
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Et recordatus est quia caro sunt: spiritus vadens, et non rediens.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Quoties exacerbaverunt eum in deserto, in iram concitaverunt eum in inaquoso?
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Et conversi sunt, et tentaverunt Deum: et Sanctum Israel exacerbaverunt.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Non sunt recordati manus eius, die qua redemit eos de manu tribulantis,
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Sicut posuit in Ægypto signa sua, et prodigia sua in campo Taneos.
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Et convertit in sanguinem flumina eorum, et imbres eorum, ne biberent.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Misit in eos cœnomyiam, et comedit eos: et ranam, et disperdidit eos.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Et dedit ærugini fructus eorum: et labores eorum locustæ.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Et occidit in grandine vineas eorum: et moros eorum in pruina.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Et tradidit grandini iumenta eorum: et possessionem eorum igni.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Misit in eos iram indignationis suæ: indignationem, et iram, et tribulationem: immissiones per angelos malos.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Viam fecit semitæ iræ suæ, non pepercit a morte animabus eorum: et iumenta eorum in morte conclusit.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Et percussit omne primogenitum in terra Ægypti: primitias omnis laboris eorum in tabernaculis Cham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Et abstulit sicut oves populum suum: et perduxit eos tamquam gregem in deserto.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Et deduxit eos in spe, et non timuerunt: et inimicos eorum operuit mare.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Et induxit eos in montem sanctificationis suæ, montem, quem acquisivit dextera eius. Et eiecit a facie eorum Gentes: et sorte divisit eis terram in funiculo distributionis.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Et habitare fecit in tabernaculis eorum tribus Israel.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Et tentaverunt, et exacerbaverunt Deum excelsum: et testimonia eius non custodierunt.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Et averterunt se, et non servaverunt pactum: quemadmodum patres eorum, conversi sunt in arcum pravum.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
In iram concitaverunt eum in collibus suis: et in sculptilibus suis ad æmulationem eum provocaverunt.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Audivit Deus, et sprevit: et ad nihilum redegit valde Israel.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Et repulit tabernaculum Silo, tabernaculum suum, ubi habitavit in hominibus.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Et tradidit in captivitatem virtutem eorum: et pulchritudinem eorum in manus inimici.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Et conclusit in gladio populum suum: et hereditatem suam sprevit.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Iuvenes eorum comedit ignis: et virgines eorum non sunt lamentatæ.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Sacerdotes eorum in gladio ceciderunt: et viduæ eorum non plorabantur.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Et excitatus est tamquam dormiens Dominus, tamquam potens crapulatus a vino.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Et percussit inimicos suos in posteriora: opprobrium sempiternum dedit illis.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Et repulit tabernaculum Ioseph: et tribum Ephraim non elegit:
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Sed elegit tribum Iuda, montem Sion quem dilexit.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Et ædificavit sicut unicornium sanctificium suum in terra, quam fundavit in sæcula.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Et elegit David servum suum, et sustulit eum de gregibus ovium: de post fœtantes accepit eum.
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Pascere Iacob servum suum, et Israel hereditatem suam:
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Et pavit eos in innocentia cordis sui: et in intellectibus manuum suarum deduxit eos.

< Zabura 78 >