< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Cantico di Asaf. Ascolta, popolo mio, il mio insegnamento; porgete gli orecchi alle parole della mia bocca!
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Io aprirò la mia bocca per proferir parabole, esporrò i misteri de’ tempi antichi.
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Quel che noi abbiamo udito e conosciuto, e che i nostri padri ci hanno raccontato,
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
non lo celeremo ai loro figliuoli; diremo alla generazione avvenire le lodi dell’Eterno, e la sua potenza e le maraviglie ch’egli ha operato.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Egli stabilì una testimonianza in Giacobbe, e pose una legge in Israele, ch’egli ordinò ai nostri padri di far conoscere ai loro figliuoli,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
perché fossero note alla generazione avvenire, ai figliuoli che nascerebbero, i quali alla loro volta le narrerebbero ai loro figliuoli,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
ond’essi ponessero in Dio la loro speranza e non dimenticassero le opere di Dio, ma osservassero i suoi comandamenti;
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
e non fossero come i loro padri, una generazione caparbia e ribelle, una generazione dal cuore incostante, e il cui spirito non fu fedele a Dio.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
I figliuoli di Efraim, gente di guerra, buoni arcieri, voltaron le spalle il dì della battaglia.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Non osservarono il patto di Dio, e ricusarono di camminar secondo la sua legge;
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
e dimenticarono le sue opere e i prodigi ch’egli avea loro fatto vedere.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Egli avea compiuto maraviglie in presenza de’ loro padri, nel paese d’Egitto, nelle campagne di Zoan.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Fendé il mare e li fece passare, e fermò le acque come in un mucchio.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Di giorno li guidò con una nuvola, e tutta la notte con una luce di fuoco.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Schiantò rupi nel deserto, e li abbeverò copiosamente, come da gorghi.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Fece scaturire ruscelli dalla roccia e ne fece scender dell’acque a guisa di fiumi.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Ma essi continuarono a peccare contro di lui, a ribellarsi contro l’Altissimo, nel deserto;
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
e tentarono Dio in cuor loro, chiedendo cibo a lor voglia.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
E parlarono contro Dio, dicendo: Potrebbe Dio imbandirci una mensa nel deserto?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Ecco, egli percosse la roccia e ne colarono acque, ne traboccaron torrenti; potrebb’egli darci anche del pane, e provveder di carne il suo popolo?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Perciò l’Eterno, avendoli uditi, s’adirò fieramente, e un fuoco s’accese contro Giacobbe, e l’ira sua si levò contro Israele,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
perché non aveano creduto in Dio, né avevano avuto fiducia nella sua salvazione;
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
eppure egli comandò alle nuvole di sopra, e aprì le porte del cielo,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
e fece piover su loro manna da mangiare, e dette loro del frumento del cielo.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
L’uomo mangiò del pane dei potenti; egli mandò loro del cibo a sazietà.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Fece levare in cielo il vento orientale, e con la sua potenza addusse il vento di mezzodì;
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
fece piover su loro della carne come polvere, degli uccelli alati, numerosi come la rena del mare;
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
e li fece cadere in mezzo al loro campo, d’intorno alle loro tende.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Così essi mangiarono e furon ben satollati, e Dio mandò loro quel che aveano bramato.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Non si erano ancora distolti dalle loro brame, avevano ancora il loro cibo in bocca,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
quando l’ira di Dio si levò contro loro, e ne uccise tra i più fiorenti, e abbatté i giovani d’Israele.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Con tutto ciò peccarono ancora, e non credettero alle sue maraviglie.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Ond’egli consumò i loro giorni in vanità, e i loro anni in ispaventi.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Quand’ei li uccideva, essi lo ricercavano e tornavano bramosi di ritrovare Iddio;
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
e si ricordavano che Dio era la loro ròcca, l’Iddio altissimo il loro redentore.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Essi però lo lusingavano con la loro bocca, e gli mentivano con la loro lingua.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Il loro cuore non era diritto verso lui, e non eran fedeli al suo patto.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Ma egli, che è pietoso, che perdona l’iniquità e non distrugge il peccatore, più volte rattenne la sua ira, e non lasciò divampare tutto il suo cruccio.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Ei si ricordò ch’essi erano carne, un fiato che passa e non ritorna.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Quante volte si ribellarono a lui nel deserto, e lo contristarono nella solitudine!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
E tornarono a tentare Iddio e a provocare il Santo d’Israele.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Non si ricordaron più della sua mano, del giorno in cui egli li liberò dal nemico,
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
quando operò i suoi miracoli in Egitto, e i suoi prodigi nelle campagne di Zoan;
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
mutò i loro fiumi in sangue, e i loro rivi in guisa che non potean più bere;
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
mandò contro loro mosche velenose che li divoravano, e rane che li distruggevano;
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
dette il loro raccolto ai bruchi e la loro fatica alle locuste;
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
distrusse le loro vigne con la gragnuola e i loro sicomori coi grossi chicchi d’essa;
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
abbandonò il loro bestiame alla grandine e le lor gregge ai fulmini.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Scatenò su loro l’ardore del suo cruccio, ira, indignazione e distretta, una torma di messaggeri di malanni.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Dette libero corso alla sua ira; non preservò dalla morte la loro anima, ma abbandonò la loro vita alla pestilenza.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Percosse tutti i primogeniti d’Egitto, le primizie del vigore nelle tende di Cham;
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
ma fece partire il suo popolo a guisa di pecore, e lo condusse a traverso il deserto come una mandra.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Lo guidò sicuramente sì che non ebbero da spaventarsi, mentre il mare inghiottiva i loro nemici.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Li fece arrivare alla sua santa frontiera, alla montagna che la sua destra avea conquistato.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Scacciò le nazioni dinanzi a loro, ne assegnò loro a sorte il paese quale eredità, e nelle tende d’esse fece abitare le tribù d’Israele.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
E nondimeno tentarono l’Iddio altissimo e si ribellarono e non osservarono le sue testimonianze.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Si trassero indietro e furono sleali come i loro padri; si rivoltarono come un arco fallace;
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
lo provocarono ad ira coi loro alti luoghi, lo mossero a gelosia con le loro sculture.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Dio udì questo, e si adirò, prese Israele in grande avversione,
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
onde abbandonò il tabernacolo di Silo, la tenda ov’era dimorato fra gli uomini;
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
e lasciò menare la sua Forza in cattività, e lasciò cader la sua Gloria in man del nemico.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Abbandonò il suo popolo alla spada, e s’adirò contro la sua eredità.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Il fuoco consumo i loro giovani, e le loro vergini non ebber canto nuziale.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
I loro sacerdoti caddero per la spada, e le loro vedove non fecer lamento.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Poi il Signore si risvegliò come uno che dormisse, come un prode che grida eccitato dal vino.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
E percosse i suoi nemici alle spalle, e mise loro addosso un eterno vituperio.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Ma ripudiò la tenda di Giuseppe, e non elesse la tribù di Efraim;
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
ma elesse la tribù di Giuda, il monte di Sion ch’egli amava.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Edificò il suo santuario a guisa de’ luoghi eccelsi, come la terra ch’egli ha fondata per sempre.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Elesse Davide, suo servitore, lo prese dagli ovili;
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
lo trasse di dietro alle pecore lattanti, per pascere Giacobbe suo popolo, ed Israele sua eredità.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Ed egli li pasturò secondo l’integrità del suo cuore, e li guidò con mano assennata.