< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Ein Maskil Asaphs. Vernimm, mein Volk, meine Unterweisung, neigt euer Ohr den Worten meines Mundes!
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Ich will meinen Mund zu Sprüchen aufthun, will Rätsel aus der Vorzeit verkünden.
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Was wir gehört und erfahren, und was unsere Väter uns erzählt haben,
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
wollen wir ihren Kindern nicht verhehlen, indem wir dem nachfolgenden Geschlechte die ruhmwürdigen Thaten Jahwes erzählen und seine Macht und die Wunder, die er gethan hat.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Er stellte ein Zeugnis in Jakob auf und gab eine Weisung in Israel, indem er unseren Vätern gebot, sie ihren Söhnen kundzuthun,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
damit das nachkommende Geschlecht sie erführe, die Söhne, die geboren würden, damit sie aufträten und ihren Söhnen davon erzählten,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
damit sie auf Gott ihr Vertrauen setzten und der großen Thaten Gottes nicht vergäßen und seine Gebote hielten
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
und nicht wie ihre Väter würden, ein abtrünniges und widerspenstiges Geschlecht, ein Geschlecht, das nicht festes Sinnes war, und dessen Geist nicht treulich an Gott hielt.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Die Söhne Ephraims, die Bogengerüsteten, kehrten am Tage des Kampfes um.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Sie hielten den Bund Gottes nicht und wollten nicht nach seinem Gesetze wandeln.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Sie vergaßen seine großen Thaten und seine Wunder, die er sie hatte schauen lassen.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Vor ihren Vätern hatte er Wunder gethan in Ägypten, im Gefilde von Zoan.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Er spaltete das Meer und ließ sie hindurchgehn und stellte die Wasser auf wie einen Damm.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Er leitete sie tagsüber mit der Wolke, die ganze Nacht hindurch mit feurigem Schein.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Er spaltete Felsen in der Wüste und tränkte sie wie mit Fluten in Fülle.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Er ließ Bäche aus dem Felsen hervorgehn und Wasser in Strömen herabfließen.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Dennoch sündigten sie weiter gegen ihn, indem sie sich in der Wüste gegen den Höchsten empörten.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Sie versuchten Gott in ihrem Herzen, indem sie Speise für ihr Gelüsten forderten.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Sie redeten wider Gott und sprachen: “Kann wohl Gott in der Wüste einen Tisch anrichten?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
“Wohl schlug er den Felsen, daß Wasser strömten, und Bäche sich ergossen; “vermag er wohl auch Brot zu geben oder seinem Volke Fleisch zu verschaffen?”
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Darum, als Jahwe das hörte, entrüstete er sich, und Feuer entzündete sich wider Jakob, und Zorn stieg herauf über Israel,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
weil sie Gotte nicht glaubten und auf seine Hilfe nicht vertrauten.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Und er gebot den Wolken droben und öffnete die Thüren des Himmels,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
ließ Manna auf sie regnen, daß sie zu essen hätten, und verlieh ihnen Himmelskorn.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Engelbrot hatte jedermann zu essen; er sandte ihnen Zehrung in Fülle.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Er ließ den Ostwind am Himmel aufbrechen und führte durch seine Stärke den Südwind herbei.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Er ließ Fleisch auf sie regnen wie Staub und beflügelte Vögel wie Sand am Meer.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Mitten in sein Lager ließ er sie fallen, rings um seine Wohnung her.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Da aßen sie und wurden gründlich satt, und er befriedigte ihr Gelüst.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Noch hatten sie sich ihres Gelüstes nicht entschlagen - sie hatten ihre Speise noch im Mund -
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
da stieg der Zorn Gottes über sie herauf und würgte unter ihren Fetten und streckte die Jünglinge Israels nieder.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Trotz alledem sündigten sie weiter und glaubten nicht an seine Wunder.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Darum ließ er ihre Tage wie einen Hauch dahinschwinden und ihre Jahre in bestürzender Schnelle.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Wenn er sie würgte, so fragten sie nach ihm und wendeten sich zurück zu Gott
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
und gedachten daran, daß Gott ihr Fels und Gott, der Höchste, ihr Erlöser sei.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Sie beschwatzten ihn mit ihrem Munde und logen ihm mit ihrer Zunge;
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
aber ihr Sinn war ihm gegenüber nicht fest, und sie hielten nicht treulich an seinem Bund,
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
während doch er barmherzig war, Schuld vergab und sie nicht vertilgte, gar oft von seinem Zorn abließ und nicht seinen ganzen Grimm aufbot.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Denn er gedachte daran, daß sie Fleisch seien, ein Hauch, der dahinfährt und nicht wiederkommt.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Wie oft empörten sie sich gegen ihn in der Wüste, betrübten sie ihn in der Einöde!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Immer wieder versuchten sie Gott und kränkten den Heiligen Israels.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Sie gedachten nicht an seine gewaltige Hand, an den Tag, da er sie vom Feinde befreit hatte,
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
da er seine Zeichen in Ägypten hinstellte und seine Wunder im Gefilde von Zoan.
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Denn er verwandelte ihre Ströme in Blut und ihre Bäche, damit sie nicht trinken könnten.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Er sandte Hundsfliegen gegen sie, die fraßen sie, und Frösche, die verderbten sie.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Er gab ihr Gewächs dem Ungeziefer preis und was sie erarbeitet, der Heuschrecke.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Er erschlug ihre Weinstöcke mit Hagel und ihre Maulbeerfeigenbäume mit Schloßen.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Er gab ihr Vieh dem Hagel preis und ihre Herden den Blitzen.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Er entsandte wider sie die Glut seines Zorns, Wut und Grimm und Drangsal, eine Schar von Unglücksengeln.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Er ließ seinem Zorne freien Lauf, entzog ihre Seele nicht dem Tod und überlieferte ihr Leben der Pest.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Er schlug alle Erstgeburt in Ägypten, die Erstlinge der Manneskraft in den Zelten Hams.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Und er ließ sein Volk ausziehen wie Schafe und leitete sie in der Wüste wie eine Herde.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Er führte sie sicher, und sie brauchten sich nicht zu fürchten; ihre Feinde aber bedeckte das Meer.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Er brachte sie in sein heiliges Gebiet, zu dem Berge, den seine Rechte erworben hatte.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Er vertrieb vor ihnen Völker, verloste ihr Land zum erblichen Besitz und ließ in ihren Zelten die Stämme Israels wohnen.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Aber sie versuchten Gott, den Höchsten, und empörten sich gegen ihn und hielten seine Gebote nicht.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Sie wandten sich ab und waren treulos wie ihre Väter, wandelten sich, wie ein trügerischer Bogen.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Sie erzürnten ihn mit ihren Höhen und erregten seinen Eifer durch ihre Bilder.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Da Gott das vernahm, entrüstete er sich und verwarf Israel völlig.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Er gab die Wohnung zu Silo preis, das Zelt, wo er unter den Menschen wohnte,
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
ließ seine Macht in die Gefangenschaft wandern und seine Zier in die Gewalt des Feindes.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Er gab sein Volk dem Schwerte preis und entrüstete sich über sein Besitztum.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Seine Jünglinge fraß das Feuer, und seine Jungfrauen blieben ohne Hochzeitslied.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Seine Priester fielen durch das Schwert, und seine Witwen hielten keine Totenklage.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Da erwachte der Herr wie ein Schlafender, wie ein Held, der vom Weine besiegt ward.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Und er schlug seine Feinde zurück: ewige Schmach brachte er über sie.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Und er verwarf das Zelt Josephs und erwählte nicht den Stamm Ephraim,
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
sondern erwählte den Stamm Juda, den Berg Zion, den er liebgewonnen.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Und er baute so fest wie die Himmelshöhen sein Heiligtum, wie die Erde, die er für die Ewigkeit gegründet hat.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Er erwählte seinen Knecht David und nahm ihn von den Schafhürden hinweg.
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Von den säugenden Schafen holte er ihn weg, daß er sein Volk Jakob weide und Israel, sein Besitztum.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Und er weidete sie in Herzenseinfalt und führte sie mit kluger Hand.

< Zabura 78 >