< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Intelligence d’Asaph.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
J’ouvrirai ma bouche en paraboles: je dirai des choses cachées dès le commencement;
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Combien de grandes choses nous avons entendu et connues, et que nos pères nous ont racontées.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Elles n’ont pas été cachées à leurs fils dans une autre génération. Ils ont raconté les louanges du Seigneur, ses œuvres puissantes, et ses merveilles qu’il a faites;
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Et a suscité un témoignage dans Jacob; et a établi une loi dans Israël: Combien de grandes choses il a commandé à nos pères de faire connaître à leurs fils,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
Afin qu’une autre génération les connaisse. Les fils qui naîtront et s’élèveront après eux les raconteront à leurs fils,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
Afin qu’ils mettent en Dieu leur espérance, qu’ils n’oublient pas ses œuvres, et qu’ils recherchent ses commandements.
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
De peur qu’ils ne deviennent comme leurs pères une génération perverse et exaspérant Dieu; Une génération qui n’a point dirigé son cœur, et dont l’esprit ne s’est point confié en Dieu.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Les fils d’Ephraïm, habiles à tendre l’arc et à en tirer, ont tourné le dos au jour du combat.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Ils n’ont pas gardé l’alliance de Dieu, et ils n’ont pas voulu marcher dans sa loi.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Ils ont oublié ses bienfaits et les merveilles qu’il leur a montrées.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Devant leurs pères il a fait des merveilles, dans la terre d’Égypte, dans la plaine de Tanis.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Il divisa la mer, et il les fit passer: et il fixa les eaux comme dans une outre.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Il les conduisit, le jour, au moyen d’une nuée, et toute la nuit à la clarté d’un feu.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Il fendit une pierre dans le désert, et les fit boire comme à un abîme abondant.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Car il fit sortir de l’eau de la pierre, et il en fit sortir des eaux comme des fleuves.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Mais ils péchèrent encore de nouveau contre lui, ils excitèrent à la colère le Très-Haut dans un lieu sans eau.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Et ils tentèrent Dieu dans leurs cœurs, au point qu’ils demandèrent une nourriture pour leurs âmes.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Et ils parlèrent mal de Dieu, ils dirent: Est-ce que Dieu pourra préparer une table dans le désert?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Parce qu’il a frappé une pierre, et que des eaux ont coulé; et que des torrents ont débordé. Est-ce qu’il pourra aussi donner du pain et préparer une table pour son peuple?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
C’est pour cela que le Seigneur entendit et différa; mais un feu s’alluma contre Jacob, et sa colère monta contre Israël;
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Parce qu’ils ne crurent pas en Dieu, et qu’ils n’espérèrent pas en son salut;
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Et il commanda aux nuées d’en haut, et il ouvrit les portes du ciel.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Et il leur fit pleuvoir de la manne pour manger, et il leur donna du pain du ciel.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
L’homme mangea le pain des anges, Dieu leur envoya une nourriture en abondance.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Il fit disparaître du ciel le vent du midi, et il amena par sa puissance le vent d’Afrique.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Il fit pleuvoir sur eux des viandes comme la poussière, et des oiseaux comme le sable de la mer.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Et ils tombèrent au milieu de leur camp, autour de leurs tabernacles.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Ils mangèrent et ils furent rassasiés à l’excès, et Dieu leur accorda selon leur désir;
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Ils ne furent point frustrés dans leur désir. Leurs viandes étaient encore dans leur bouche,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
Quand la colère de Dieu tomba sur eux. Et il tua les gras d’entre eux, et rejeta l’élite d’Israël.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Au milieu de tous ces prodiges ils péchèrent encore, et ne crurent pas à ses merveilles.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Et leurs jours se terminèrent vainement, et leurs années avec rapidité.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Lorsqu’il les tuait, ils le cherchaient, et ils revenaient, et, dès le point du jour, ils venaient à lui.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Et ils se souvinrent que Dieu était leur aide, et que le Dieu très haut était leur rédempteur.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Mais ils l’aimèrent de bouche seulement, et ils lui mentirent par leur langue;
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Car leur cœur n’était pas droit avec lui, et ils ne furent pas trouvés fidèles à son alliance.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Mais lui est miséricordieux, il pardonnera leurs péchés, et ne les perdra pas entièrement. Et souvent il détourna sa colère, et il n’alluma pas toute sa colère.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Il se rappela qu’ils étaient chair, un souffle qui va et qui ne revient pas.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Combien de fois l’ont-ils irrité dans le désert, et l’ont-ils excité à la colère dans un lieu sans eau?
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Et de nouveau ils tentèrent Dieu, et ils ont aigri le saint d’Israël.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Ils ne se sont pas rappelé sa main, au jour où il les retira de la main d’un oppresseur,
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Comment il fit en Égypte ses miracles, et ses prodiges dans la plaine de Tanis.
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Et il changea en sang leurs fleuves et leurs pluies, pour qu’ils ne bussent point.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Il envoya contre eux une multitude de mouches qui les dévorèrent, et la grenouille qui les ravagea.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Et il donna à la rouille leurs fruits, et leurs travaux à la sauterelle.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Et il fit périr par la grêle leurs vignes, et leurs mûriers par la gelée.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Et il livra à la grêle leurs bêtes, et leurs possessions au feu.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Il envoya contre eux la colère de son indignation: l’indignation, et la colère, et la tribulation envoyées par des anges mauvais.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Il fit une voie au sentier de sa colère, et il n’épargna pas la mort à leurs âmes; et leurs bêtes, il les renferma dans la mort.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Et il frappa tout premier-né d’Égypte, les prémices de tout travail dans les tabernacles de Cham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Et il en retira, comme des brebis, son peuple; et il les conduisit comme un troupeau dans le désert.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Et il les fit sortir pleins d’espérance, et ils ne craignirent point; quant à leurs ennemis, la mer les couvrit.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Et il les amena sur la montagne de sa sanctification; montagne qu’a acquise sa droite. Et il chassa de leur face des nations; et il leur divisa au sort une terre avec un cordeau de partage.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Et il fit habiter dans leurs tabernacles les tribus d’Israël.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Mais ils tentèrent et aigrirent le Dieu très haut; et ne gardèrent pas ses témoignages.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Et ils se détournèrent de lui et n’observèrent pas l’alliance; de la même manière que leurs pères, ils devinrent comme un arc qui porte à faux.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Ils l’ont excité à la colère sur leurs collines; et par leurs images taillées au ciseau, ils l’ont provoqué à la jalousie.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Dieu entendit, et il méprisa, et il réduisit entièrement au néant Israël.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Et il repoussa le tabernacle de Silo, son tabernacle où il avait habité parmi les hommes.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Il livra à la captivité l’arche, leur force; et leur beauté entre les mains de l’ennemi.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Il renferma son peuple entre les glaives; et son héritage, il le méprisa.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Un feu dévora leurs jeunes hommes; et leurs vierges ne furent pas pleurées.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Leurs prêtres tombèrent sous le glaive, et on ne pleurait pas leurs veuves.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Mais le Seigneur se réveilla comme un homme endormi, comme un héros qui a été ivre de vin.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Il frappa ses ennemis par derrière; il leur infligea un opprobre éternel.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Et il repoussa le tabernacle de Joseph, et ne choisit point la tribu d’Éphraïm;
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Mais il choisit la tribu de Juda, la montagne de Sion qu’il a aimée.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Et il bâtit comme une corne de licornes son sanctuaire, dans la terre qu’il a fondée pour les siècles.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Il choisit David son serviteur, et il le tira du milieu des troupeaux de brebis: il le prit à la suite de celles qui étaient pleines,
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Pour être le pasteur de Jacob son serviteur, et d’Israël son héritage.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Et David les fit paître dans l’innocence de son cœur, et avec ses mains habiles, il les conduisit.