< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Maskîl d’Assaph. Ecoute, ô mon peuple, mon enseignement, prête l’oreille aux paroles de ma bouche.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
J’Ouvre les lèvres pour des sentences poétiques, j’énonce des aphorismes venant des temps anciens.
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Ce que nous connaissons pour l’avoir entendu, ce que nos pères nous ont raconté,
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
nous ne le laissons pas ignorer à leurs descendants; à la génération la plus reculée nous voulons raconter les œuvres glorieuses de l’Eternel, sa puissance et les merveilles qu’il a accomplies.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Il a établi un code dans Jacob, institué une loi en Israël; et il ordonna à nos pères de les enseigner à leurs enfants,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
pour que la génération future soit mise au courant, pour que les enfants qui viendraient à naître se lèvent et à leur tour en instruisent leurs fils.
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
Qu’ils mettent donc leur confiance en Dieu, se gardent d’oublier les hauts faits du Tout-Puissant, et observent ses prescriptions!
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
Et qu’ils ne soient pas, comme leurs ancêtres, une génération insoumise et rebelle, une génération au cœur inconstant et à l’esprit non sincèrement fidèle à Dieu.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Les fils d’Ephraïm, armés de l’arc, habiles tireurs, ont tourné le dos au jour du combat!
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Ils ont répudié l’alliance de Dieu et refusé de suivre sa loi.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Ils ont oublié ses grandes œuvres et ses merveilles, dont il les avait rendus témoins.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Sous les yeux de leurs pères il accomplit des prodiges, sur la terre d’Egypte, dans les champs de Çoân.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Il fendit la mer pour leur ouvrir un passage, fit se dresser les ondes comme une digue.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Le jour, il les dirigeait au moyen de la nuée, et toute la nuit, par l’éclat du feu.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Il entrouvrit des roches dans le désert, et offrit à leur soif des flots abondants.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Il fit jaillir des torrents du granit et couler les eaux comme des fleuves.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Mais ils continuèrent à pécher contre lui, à s’insurger contre le Très-Haut dans ces régions arides.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Au fond de leur cœur, ils mirent Dieu à l’épreuve, en demandant une nourriture selon leur goût.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Ils tinrent des propos contre Dieu, disant:
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
"Dieu pourra-t-il dresser une table dans le désert? Sans doute il a frappé un rocher, et les eaux ont jailli, des torrents se sont précipités: pourra-t-il aussi donner du pain? Sera-t-il capable d’apprêter de la viande à son peuple?"
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
C’Est pourquoi l’Eternel, les ayant entendus, s’irrita; un feu s’alluma contre Jacob, et sa colère s’éleva contre Israël,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
parce qu’ils n’avaient pas eu foi en Dieu, ni témoigné de leur confiance en son secours.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Il commanda aux nuages d’en haut, et ouvrit les portes du ciel.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Il fit pleuvoir sur eux de la manne comme nourriture, et leur octroya du blé céleste.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Tous eurent à manger de ce pain de délices: il leur avait envoyé des vivres à satiété.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Puis il abattit le vent d’Est sous les cieux, et sa puissance déchaîna le vent du Midi.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Il fit pleuvoir sur eux de la viande dru comme la poussière, des oiseaux ailés nombreux comme le sable de la mer;
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
il les fit tomber au milieu de leur camp, tout autour de leurs tentes.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Ils mangèrent et furent pleinement rassasiés: il leur accorda l’objet de leur convoitise.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Eux n’avaient pas encore assouvi leur désir, la nourriture était encore dans leur bouche,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
que la colère de Dieu s’éleva contre eux; il en décima les plus vigoureux et coucha à terre les gens d’élite en Israël.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Malgré cela ils péchèrent encore, et n’ajoutèrent point foi à ses merveilles.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Il mit donc fin à leurs jours par un souffle, à leurs années par des coups soudains.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Quand il les faisait ainsi périr, ils le recherchaient; venant à résipiscence, ils se mettaient en quête de Dieu.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Alors ils se souvenaient que Dieu était leur rocher, le Dieu suprême leur libérateur.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Ils l’amadouaient avec leur bouche, en paroles ils lui offraient des hommages menteurs,
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
mais leur cœur n’était pas de bonne foi à son égard; ils n’étaient pas sincèrement attachés à son alliance.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Mais lui, plein de miséricorde, pardonne les fautes, pour ne pas consommer des ruines; bien souvent il laisse sa colère s’apaiser, et n’a garde de déchaîner tout son courroux.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Il se souvint donc que c’étaient de faibles créatures, un souffle qui s’évanouit sans retour.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Que de fois ils s’insurgèrent contre lui dans le désert et l’offensèrent dans ces lieux solitaires!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Ils revenaient sans cesse à la charge, mettant à l’épreuve le Tout-Puissant, et défiant le Saint d’Israël.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Ils étaient oublieux de sa puissance, oublieux du jour où il les délivra de l’ennemi;
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
car il fit éclater ses prodiges en Egypte, et ses miracles dans les champs de Çoân.
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Il changea en sang leurs fleuves, et leurs cours d’eau ne furent plus potables.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Il lança contre eux des bêtes malfaisantes pour les dévorer, des grenouilles pour les ruiner.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Il livra leurs plantations aux locustes, et le produit de leur travail aux sauterelles.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Par la grêle il fit périr leurs vignes, et leurs sycomores par les giboulées.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Il abandonna leur bétail en proie à la grêle, et leurs troupeaux aux ravages de la foudre.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Il lâcha sur eux le feu de sa colère, courroux, malédiction et fléaux, tout un essaim d’anges malfaisants.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Il donna libre cours à sa colère, ne les préserva pas eux-mêmes de la mort, mais les fit succomber, victimes de la peste.
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Il frappa tout premier-né en Egypte, les prémices de leur vigueur dans les tentes de Cham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Il mit en marche son peuple comme des brebis, et les conduisit comme un troupeau dans le désert.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Il les fit avancer en sécurité, sans qu’ils eussent rien à craindre, alors que la mer s’était refermée sur leurs ennemis.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Il les amena sur son saint territoire, sur cette montagne acquise par sa droite.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Il chassa des peuplades devant eux, leur en distribua le pays par lots héréditaires, et établit dans leurs tentes les tribus d’Israël.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Mais, redevenus rebelles, ils tentèrent le Dieu suprême, et cessèrent d’observer ses statuts.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Ils se dévoyèrent, devinrent infidèles comme leurs pères, se retournèrent comme un arc perfide.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Ils irritèrent Dieu par leurs hauts lieux, et, par leurs images sculptées, allumèrent sa jalousie.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Dieu entendit et s’emporta, eut un profond dégoût d’Israël.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Il délaissa la résidence de Silo, le tabernacle qu’il avait établi parmi les hommes.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Il laissa s’en aller en captivité sa puissance, et sa gloire tomber entre les mains de l’ennemi.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Il livra son peuple au glaive, et s’emporta contre son héritage.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Ses jeunes gens, le feu les dévora, ses jeunes filles ne connurent aucun chant d’hyménée.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Ses prêtres tombèrent par l’épée, et ses veuves ne pleurèrent point.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Alors le Seigneur se réveilla, tel un homme qui a dormi, tel un guerrier exalté par le vin.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Ses coups firent reculer ses adversaires: il leur infligea un opprobre éternel.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Mais il rejeta le tabernacle de Joseph, et cessa de préférer la tribu d’Ephraïm.
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Il porta son choix sur la tribu de Juda, sur le mont Sion, qu’il avait pris en affection;
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
il bâtit son sanctuaire, solide comme les hauteurs célestes, comme la terre qu’il a fondée pour l’éternité.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Il élut David, son serviteur, et lui fit quitter les parcs des troupeaux.
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Du milieu des brebis allaitant leurs petits, il l’amena pour être le pasteur de Jacob, son peuple, et d’Israël, son héritage.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Et lui, David, fut leur pasteur selon l’intégrité de son cœur, et les dirigea d’une main habile.