< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Pour instruire. D’Asaph. Prête l’oreille à ma loi, mon peuple! inclinez vos oreilles aux paroles de ma bouche.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
J’ouvrirai ma bouche en paraboles, j’annoncerai les énigmes [des jours] d’autrefois,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
Que nous avons entendues et connues, et que nos pères nous ont racontées.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Nous ne les cèlerons pas à leurs fils; nous raconterons à la génération à venir les louanges de l’Éternel, et sa force, et ses merveilles qu’il a faites.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Il a établi un témoignage en Jacob, et il a mis en Israël une loi qu’il a commandée à nos pères, pour qu’ils les fassent connaître à leurs fils,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
Afin que la génération à venir, les fils qui naîtraient, les connaissent, [et] qu’ils se lèvent et les annoncent à leurs fils,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
Et qu’ils mettent leur confiance en Dieu, et qu’ils n’oublient pas les œuvres de Dieu, et qu’ils observent ses commandements,
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
Et qu’ils ne soient pas, comme leurs pères, une génération indocile et rebelle, une génération qui n’a point affermi son cœur, et dont l’esprit n’a pas été fidèle à Dieu.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Les fils d’Éphraïm, armés [et] tirant de l’arc, ont tourné le dos le jour du combat.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Ils n’ont pas gardé l’alliance de Dieu, et ont refusé de marcher selon sa loi;
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Et ils ont oublié ses actes et ses œuvres merveilleuses, qu’il leur avait fait voir.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Il fit des merveilles devant leurs pères dans le pays d’Égypte, dans la campagne de Tsoan.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Il fendit la mer, et les fit passer: il fit se dresser les eaux comme un monceau;
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Et il les conduisit, le jour par une nuée, et toute la nuit par une lumière de feu.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Il fendit les rochers dans le désert, et les abreuva comme aux abîmes, abondamment;
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Et il fit sortir des ruisseaux du rocher, et fit couler les eaux comme des fleuves.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Et ils péchèrent de nouveau contre lui, irritant le Très-haut dans le désert;
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Et ils tentèrent Dieu dans leurs cœurs, en demandant de la viande selon leur désir;
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Et ils parlèrent contre Dieu; ils dirent: Dieu pourrait-il dresser une table dans le désert?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Voici, il a frappé le rocher, et les eaux ont coulé, et des rivières ont débordé: pourrait-il aussi donner du pain, ou préparer de la chair à son peuple?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
C’est pourquoi l’Éternel les entendit, et se mit en grande colère; et le feu s’alluma contre Jacob, et la colère aussi monta contre Israël,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
Car ils ne crurent pas Dieu, et ne se fièrent pas en son salut,
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Bien qu’il ait commandé aux nuées d’en haut, et qu’il ait ouvert les portes des cieux,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Et qu’il ait fait pleuvoir sur eux la manne pour manger, et qu’il leur ait donné le blé des cieux:
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
L’homme mangea le pain des puissants; il leur envoya des vivres à satiété.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Il fit lever dans les cieux le vent d’orient, et il amena par sa puissance le vent du midi;
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Et il fit pleuvoir sur eux de la chair comme de la poussière, et, comme le sable des mers, des oiseaux ailés;
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Et il les fit tomber au milieu de leur camp, autour de leurs demeures.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Et ils en mangèrent, et en furent abondamment rassasiés. Il leur envoya ce qu’ils convoitaient.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Ils ne s’étaient pas encore détournés de leur convoitise, leur viande était encore dans leur bouche,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
Que la colère de Dieu monta contre eux; et il tua de leurs hommes forts, et abattit les hommes d’élite d’Israël.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Avec tout cela ils péchèrent encore, et ne crurent point par ses œuvres merveilleuses;
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Et il consuma leurs jours par la vanité, et leurs années par la frayeur.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
S’il les tuait, alors ils le recherchaient, et ils se retournaient, et cherchaient Dieu dès le matin;
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Et ils se souvenaient que Dieu était leur rocher, et Dieu, le Très-haut, leur rédempteur;
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Mais ils le flattaient de leur bouche et ils lui mentaient de leur langue;
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Et leur cœur n’était pas ferme envers lui, et ils ne furent pas fidèles dans son alliance.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Mais lui, étant miséricordieux, pardonna l’iniquité et ne [les] détruisit pas; mais il détourna souvent sa colère, et n’éveilla pas toute sa fureur.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Et il se souvint qu’ils étaient chair, un souffle qui passe et ne revient pas.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Que de fois ils l’irritèrent dans le désert, [et] le provoquèrent dans le lieu désolé!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Et ils recommencèrent et tentèrent Dieu, et affligèrent le Saint d’Israël:
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Ils ne se souvinrent pas de sa main au jour où il les avait délivrés de l’oppresseur,
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
Lorsqu’il mit ses signes en Égypte, et ses prodiges dans les campagnes de Tsoan,
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
Et qu’il changea en sang leurs canaux et leurs courants d’eau, de sorte qu’ils n’en puissent pas boire;
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Il envoya contre eux des mouches qui les dévorèrent, et des grenouilles qui les détruisirent;
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Et il livra leurs fruits à la locuste, et leur travail à la sauterelle.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Il fit périr leurs vignes par la grêle, et leurs sycomores par les grêlons;
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Et il livra leur bétail à la grêle, et leurs troupeaux à la foudre.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Il envoya sur eux l’ardeur de sa colère, la fureur, et l’indignation, et la détresse, une troupe d’anges de malheur.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Il fraya un chemin à sa colère; il ne préserva pas leurs âmes de la mort, et livra leur vie à la peste;
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
Et il frappa tout premier-né en Égypte, les prémices de la vigueur dans les tentes de Cham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Et il fit partir son peuple comme des brebis, et les mena comme un troupeau dans le désert;
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Et il les conduisit sains et saufs, et ils furent sans crainte; et la mer couvrit leurs ennemis.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Et il les introduisit dans les confins de sa sainte [terre], cette montagne que sa droite s’est acquise.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Et il chassa de devant eux les nations, et leur partagea un héritage, et fit habiter dans leurs tentes les tribus d’Israël.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Mais ils tentèrent et irritèrent le Dieu Très-haut, et ne gardèrent pas ses témoignages,
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Et se retirèrent, et agirent infidèlement, comme leurs pères; ils tournèrent comme un arc trompeur.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Et ils le provoquèrent à colère par leurs hauts lieux, et l’émurent à jalousie par leurs images taillées.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Dieu l’entendit, et se mit en grande colère, et il méprisa fort Israël.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Et il abandonna la demeure de Silo, la tente où il avait habité parmi les hommes;
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Et il livra à la captivité sa force, et sa magnificence en la main de l’ennemi;
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Et il livra son peuple à l’épée, et se mit en grande colère contre son héritage:
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Le feu dévora leurs jeunes hommes, et leurs vierges ne furent pas célébrées;
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Leurs sacrificateurs tombèrent par l’épée, et leurs veuves ne se lamentèrent pas.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Alors le Seigneur s’éveilla comme un homme qui dort, et comme un homme puissant qui, [animé] par le vin, pousse des cris.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Et il frappa ses ennemis par-derrière, il les livra à un opprobre éternel.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Et il méprisa la tente de Joseph, et ne choisit pas la tribu d’Éphraïm;
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Mais il choisit la tribu de Juda, la montagne de Sion qu’il aima.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Et il bâtit son sanctuaire comme des lieux très hauts, comme la terre qu’il a fondée pour toujours.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Et il choisit David, son serviteur, et le prit des parcs des brebis;
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
Il le fit venir d’auprès des brebis qui allaitent, pour paître Jacob, son peuple, et Israël, son héritage.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Et il les fit paître selon l’intégrité de son cœur, et les conduisit par l’intelligence de ses mains.