< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Une contemplation d'Asaph. Écoutez mon enseignement, mon peuple. Prêtez l'oreille aux paroles de ma bouche.
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
J'ouvrirai ma bouche en une parabole. Je vais prononcer les sombres paroles de l'ancien temps,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
que nous avons entendus et connus, et nos pères nous l'ont dit.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Nous ne les cacherons pas à leurs enfants, raconter à la génération à venir les louanges de Yahvé, sa force, et les merveilles qu'il a faites.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Car il a établi une alliance en Jacob, et a nommé un enseignant en Israël, qu'il a ordonné à nos pères, qu'ils doivent les faire connaître à leurs enfants;
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
afin que la génération à venir sache, même les enfants qui doivent naître; qui doivent se lever et le dire à leurs enfants,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
afin qu'ils mettent leur espoir en Dieu, et ne pas oublier les actions de Dieu, mais gardez ses commandements,
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
et ne seront pas comme leurs pères... une génération têtue et rebelle, une génération qui n'a pas rendu son cœur loyal, dont l'esprit n'était pas ferme avec Dieu.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Les fils d'Ephraïm, armés et portant des arcs, a fait marche arrière au jour de la bataille.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Ils n'ont pas respecté l'alliance de Dieu, et ont refusé de marcher dans sa loi.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Ils ont oublié ses actions, les merveilles qu'il leur avait montrées.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Il a fait des choses merveilleuses aux yeux de leurs pères, dans le pays d'Égypte, dans les champs de Zoan.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Il fendit la mer, et les fit passer. Il a fait en sorte que les eaux se dressent comme un tas.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Pendant le jour, il les conduisait aussi avec une nuée, et toute la nuit avec une lumière de feu.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Il a fendu des rochers dans le désert, et leur donnait à boire en abondance comme dans les profondeurs.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Il a aussi fait jaillir des ruisseaux du rocher, et a fait couler les eaux comme des rivières.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Pourtant, ils ont continué à pécher contre lui, pour se rebeller contre le Très-Haut dans le désert.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Ils ont tenté Dieu dans leur cœur en demandant de la nourriture selon leur désir.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Oui, ils ont parlé contre Dieu. Ils ont dit: « Dieu peut-il préparer une table dans le désert?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Voici, il a frappé le rocher, et les eaux ont jailli, et les ruisseaux ont débordé. Peut-il aussi donner du pain? Fournira-t-il de la viande à son peuple? »
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Yahvé entendit et se mit en colère. Un feu a été allumé contre Jacob, La colère est aussi montée contre Israël,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
parce qu'ils ne croyaient pas en Dieu, et n'avait pas confiance en son salut.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Pourtant, il a commandé les cieux en haut, et a ouvert les portes du ciel.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Il fit pleuvoir sur eux la manne pour qu'ils la mangent, et leur a donné de la nourriture venant du ciel.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
L'homme a mangé le pain des anges. Il leur a envoyé de la nourriture à satiété.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Il fit souffler dans le ciel le vent d'est. Par son pouvoir, il a guidé le vent du sud.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Il a aussi fait pleuvoir sur eux de la viande comme de la poussière, des oiseaux ailés comme le sable des mers.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Il les fit tomber au milieu de leur camp, autour de leurs habitations.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Ils mangèrent donc, et furent rassasiés. Il leur a donné leur propre désir.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Ils ne se sont pas détournés de leurs envies. Leur nourriture était encore dans leur bouche,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
quand la colère de Dieu s'est élevée contre eux, a tué certains de leurs plus forts, et a frappé les jeunes hommes d'Israël.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Malgré tout cela, ils ont péché, et ne croyaient pas en ses merveilles.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
C'est pourquoi il a consumé leurs jours dans la vanité, et leurs années de terreur.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Quand il les a tués, ils ont demandé après lui. Ils sont revenus et ont cherché Dieu avec ardeur.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Ils se sont souvenus que Dieu était leur rocher, le Dieu Très-Haut, leur rédempteur.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Mais ils l'ont flatté de leur bouche, et lui ont menti avec leur langue.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Car leur cœur n'était pas droit avec lui, ils n'ont pas été fidèles à son alliance.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Mais lui, qui est miséricordieux, pardonna l'iniquité et ne les détruisit pas. Oui, plusieurs fois, il a détourné sa colère, et n'a pas déclenché toute sa colère.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Il s'est souvenu qu'ils n'étaient que chair, un vent qui passe et ne revient pas.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Combien de fois se sont-ils rebellés contre lui dans le désert, et l'ont affligé dans le désert!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Ils se retournèrent et tentèrent Dieu, et ont provoqué le Saint d'Israël.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Ils ne se sont pas souvenus de sa main, ni le jour où il les a rachetés à l'adversaire;
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
comment il a placé ses signes en Égypte, ses merveilles dans le champ de Zoan,
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
il a changé leurs fleuves en sang, et leurs ruisseaux, de sorte qu'ils ne pouvaient pas boire.
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
Il envoya parmi eux des nuées de mouches, qui les dévorèrent; et des grenouilles, qui les ont détruits.
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
Il a aussi donné leur accroissement à la chenille, et leur travail à la sauterelle.
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
Il a détruit leurs vignes par la grêle, leurs figuiers sycomores avec le gel.
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
Il a aussi livré leur bétail à la grêle, et leurs troupeaux à de chauds coups de foudre.
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
Il a jeté sur eux l'ardeur de sa colère, la colère, l'indignation et le trouble, et une bande d'anges du mal.
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
Il a tracé un chemin pour sa colère. Il n'a pas épargné leur âme de la mort, mais ont donné leur vie à la peste,
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
et frappa tous les premiers-nés d'Égypte, le chef de leur force dans les tentes de Ham.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Mais il a conduit son propre peuple comme des moutons, et les a guidés dans le désert comme un troupeau.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Il les a conduits en toute sécurité, de sorte qu'ils n'ont pas eu peur, mais la mer a submergé leurs ennemis.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Il les amena jusqu'à la frontière de son sanctuaire, à cette montagne, que sa main droite avait prise.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Il a aussi chassé les nations devant eux, les a attribués en héritage par ligne, et a fait habiter les tribus d'Israël dans leurs tentes.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Pourtant, ils ont tenté et se sont rebellés contre le Dieu Très-Haut, et n'a pas gardé ses témoignages,
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
mais ils se sont détournés, et ont agi avec perfidie comme leurs pères. Ils étaient tordus comme un arc trompeur.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Car ils l'ont irrité par leurs hauts lieux, et l'ont rendu jaloux avec leurs images gravées.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Lorsque Dieu a entendu cela, il s'est mis en colère, et abhorrait fortement Israël,
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
de sorte qu'il abandonna la tente de Silo, la tente qu'il a placée parmi les hommes,
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
et a livré sa force en captivité, sa gloire dans la main de l'adversaire.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Il a aussi livré son peuple à l'épée, et était en colère contre son héritage.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Le feu a dévoré leurs jeunes hommes. Leurs vierges n'ont pas eu de chanson de mariage.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Leurs prêtres sont tombés par l'épée, et leurs veuves ne pouvaient pas pleurer.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Alors le Seigneur se réveilla comme quelqu'un qui sort du sommeil, comme un homme puissant qui crie à cause du vin.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Il a frappé ses adversaires en arrière. Il les a soumis à un reproche perpétuel.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
De plus, il rejeta la tente de Joseph, et n'a pas choisi la tribu d'Ephraïm,
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
Mais il choisit la tribu de Juda, Le mont Sion qu'il aimait.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Il a construit son sanctuaire comme les hauteurs, comme la terre qu'il a établie pour toujours.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Il a aussi choisi David, son serviteur, et l'ont pris dans les bergeries;
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
de suivre les brebis qui ont leurs petits, il l'a amené à être le berger de Jacob, son peuple, et Israël, son héritage.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Il a doncété leur berger selon l'intégrité de son cœur, et les a guidés par l'habileté de ses mains.