< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Mit Folk! vend dine Øren til min Lære, bøjer eders Øren til min Munds Tale!
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Jeg vil oplade min Mund med Ordsprog, jeg vil udgyde mørke Taler fra fordums Tid,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
dem, som vi have hørt og vide, og vore Fædre have fortalt os.
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
Dette ville vi ikke dølge for deres Børn, for den Slægt, som kommer herefter, men forkynde Herrens megen Pris og hans Styrke og hans underfulde Gerninger, som han har gjort.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Han oprettede et Vidnesbyrd i Jakob og satte en Lov i Israel, i hvilken han bød vore Fædre at kundgøre dem for deres Børn,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
paa det den Slægt, som kom herefter, de Børn, som skulde fødes, kunde vide det, at de kunde staa op og fortælle det for deres Børn,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
og at de maatte sætte deres Haab paa Gud og ikke glemme Guds Gerninger, men bevare hans Bud;
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
og at de ikke skulde vorde som deres Fædre, en modvillig og genstridig Slægt, en Slægt, som ikke beredte sit Hjerte, og hvis Aand ikke holdt trofast ved Gud.
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
Efraims Børn vare rustede Bueskytter, men svigtede paa Stridens Dag.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
De holdt ikke Guds Pagt og vægrede sig ved at vandre i hans Lov.
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
Og de glemte hans Gerninger og hans underfulde Ting, som han havde ladet dem se.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
For deres Fædre havde han gjort Undere i Ægyptens Land, paa Zoans Mark.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Han adskilte Havet og lod dem gaa igennem og optaarnede Vandet som en Dynge.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Og han ledede dem om Dagen ved Skyen og den ganske Nat ved Ildens Lys.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Han kløvede Klipper i Ørken og gav dem at drikke som af store Dyb.
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
Og han lod Bække strømme frem af Klippen og lod Vand rinde ned som Floder.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Men de bleve endnu ved med at synde imod ham, med at være genstridige imod den Højeste i Ørken.
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
Og de fristede Gud i deres Hjerte, saa at de begærede Mad for deres Lyst.
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
Og de talte imod Gud; de sagde: Mon Gud kan berede et Bord i Ørken?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Se, han har slaget Klippen, saa at der flød Vand, og Bækkene løb over; mon han og kan give Brød; mon han kan skaffe Kød for sit Folk?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Derfor, da Herren hørte det, blev han fortørnet; og en Ild optændtes imod Jakob, og en Vrede opkom imod Israel,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
fordi de ikke troede paa Gud og ikke forlode sig paa hans Frelse.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Og han bød Skyerne heroventil og oplod Himlenes Døre.
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
Og han lod Man regne paa dem til at æde og gav dem Himmelkorn.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Hver aad de stærkes Brød; han sendte dem Mad til Mættelse.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Han lod Østenvejr fare frem under Himmelen og førte Søndenvejr frem ved sin Styrke.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Og han lod Kød regne ned over dem som Støv og flyvende Fugle som Havets Sand.
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
Og han lod dem falde midt i sin Lejr, trindt omkring sine Boliger.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Og de aade og bleve saare mætte; han tilførte dem det, som de havde faaet Lyst til.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
De havde ikke styret deres Lyst, deres Mad var endnu i deres Mund:
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
Da opsteg Guds Vrede imod dem, og han ihjelslog nogle iblandt de kraftigste af dem; og han nedslog de unge Mænd i Israel.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Med alt det syndede de endnu og troede ikke paa hans underfulde Gerninger.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Derfor lod han deres Dage svinde hen i Forfængelighed og deres Aar i Forskrækkelse.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Naar han slog dem ihjel, da søgte de ham, og de vendte om og søgte Gud aarle.
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Og de kom i Hu, at Gud var deres Klippe, og Gud, den Højeste, deres Genløser.
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
Men de talte slesk for ham med deres Mund og løj for ham med deres Tunger.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Men deres Hjerte var ikke fast med ham, og de bleve ikke bestandige i hans Pagt.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Dog, han er barmhjertig, han soner Misgerning og fordærver ikke; han vendte sin Vrede mangfoldige Gange bort fra dem og lod ej sin Harme helt bryde frem.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Og han kom i Hu, at de vare Kød, et Aandepust, som farer hen og ej kommer tilbage.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Hvor tit vare de genstridige imod ham i Ørken, bedrøvede ham i de øde Steder.
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Og de fristede Gud paany og mestrede den Hellige i Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
De kom ikke hans Haand i Hu paa den Dag, da han udløste dem af Nød;
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
da han satte sine Tegn i Ægypten og sine Undere paa Zoans Mark;
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
da han forandrede deres Floder til Blod og deres Strømme, saa at de ikke kunde drikke af dem;
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
og han sendte alle Haande Utøj paa dem, som aad dem, og Frøer, som voldte dem Fordærvelse;
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
og han gav Kornormen deres Grøde og Græshoppen deres Arbejde;
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
han slog deres Vintræer med Hagelen og deres Morbærtræer med Isstykker;
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
og han overantvordede deres Dyr til Hagelen og deres Kvæg til Lynene;
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
han sendte sin grumme Vrede paa dem, Harme og Fortørnelse og Angest, en Sending af Ulykkesbud;
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
han banede Vej for sin Vrede, han sparede ikke deres Sjæl fra Døden, og han overantvordede deres Liv til Pesten;
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
og han slog alle førstefødte i Ægypten, Kraftens Førstegrøde i Kams Telte;
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
men sit Folk lod han drage ud som Faareflokken og førte dem i Ørken som Hjorden;
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
og han ledede dem tryggelig, at de ikke flygtede; men Havet skjulte deres Fjender.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Og han førte dem til sin Helligheds Landemærke, til dette Bjerg, som hans højre Haand havde forhvervet;
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
og han uddrev Hedningerne for deres Ansigt og lod disses Land tilfalde dem som Arvedel; og han lod Israels Stammer bo i deres Telte.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Men de fristede Gud, den Højeste, og vare genstridige imod ham og agtede ikke paa hans Vidnesbyrd.
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
Og de vendte sig bort og bleve troløse som deres Fædre, de sloge tilbage som en falsk Bue.
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
Og de opirrede ham ved deres Høje og gjorde ham nidkær ved deres udskaarne Billeder.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Der Gud det hørte, da blev han fortørnet, og han foragtede Israel saare.
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
Han forlod Boligen i Silo, det Paulun, som han havde sat til at bo udi iblandt Menneskene.
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
Og han gav sin Magt i Fangenskab og sin Herlighed i Fjendens Haand.
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
Og han overantvordede sit Folk til Sværd og fortørnedes paa sin Arv.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Ild fortærede deres unge Mandskab, og deres Jomfruer fik ingen Brudesang.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Deres Præster faldt for Sværdet, og deres Enker begræd dem ikke.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Da opvaagnede Herren som en sovende, som en Helt, der jubler af Vin.
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
Og han slog sine Fjender tilbage, han gjorde dem en evig Skam.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Og han forkastede Josefs Telt og udvalgte ikke Efraims Stamme;
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
men han udvalgte Judas Stamme, Zions Bjerg, som han elskede.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Og han byggede sin Helligdom lig Højderne, lig Jorden, hvilke han har grundfæstet evindelig.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Og han udvalgte David, sin Tjener, og tog ham fra Faarestierne;
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
fra Faarene, som gave Die, lod han ham komme at vogte Jakob sit Folk og Israel sin Arv.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Og han vogtede dem efter sit Hjertes Oprigtighed og ledede dem med forstandig Haand.

< Zabura 78 >