< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
亚萨的训诲诗。 我的民哪,你们要留心听我的训诲, 侧耳听我口中的话。
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
我要开口说比喻; 我要说出古时的谜语,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
是我们所听见、所知道的, 也是我们的祖宗告诉我们的。
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
我们不将这些事向他们的子孙隐瞒, 要将耶和华的美德和他的能力, 并他奇妙的作为,述说给后代听。
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
因为,他在雅各中立法度, 在以色列中设律法; 是他吩咐我们祖宗要传给子孙的,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
使将要生的后代子孙可以晓得; 他们也要起来告诉他们的子孙,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
好叫他们仰望 神, 不忘记 神的作为, 惟要守他的命令。
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
不要像他们的祖宗, 是顽梗悖逆、居心不正之辈, 向着 神,心不诚实。
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
以法莲的子孙带着兵器,拿着弓, 临阵之日转身退后。
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
他们不遵守 神的约, 不肯照他的律法行;
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
又忘记他所行的 和他显给他们奇妙的作为。
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
他在埃及地,在琐安田, 在他们祖宗的眼前施行奇事。
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
他将海分裂,使他们过去, 又叫水立起如垒。
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
他白日用云彩, 终夜用火光引导他们。
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
他在旷野分裂磐石, 多多地给他们水喝,如从深渊而出。
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
他使水从磐石涌出, 叫水如江河下流。
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
他们却仍旧得罪他, 在干燥之地悖逆至高者。
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
他们心中试探 神, 随自己所欲的求食物,
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
并且妄论 神说: 神在旷野岂能摆设筵席吗?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
他曾击打磐石,使水涌出,成了江河; 他还能赐粮食吗? 还能为他的百姓预备肉吗?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
所以,耶和华听见就发怒; 有烈火向雅各烧起; 有怒气向以色列上腾;
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
因为他们不信服 神, 不倚赖他的救恩。
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
他却吩咐天空, 又敞开天上的门,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
降吗哪,像雨给他们吃, 将天上的粮食赐给他们。
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
各人吃大能者的食物; 他赐下粮食,使他们饱足。
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
他领东风起在天空, 又用能力引了南风来。
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
他降肉,像雨在他们当中,多如尘土, 又降飞鸟,多如海沙,
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
落在他们的营中, 在他们住处的四面。
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
他们吃了,而且饱足; 这样就随了他们所欲的。
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
他们贪而无厌, 食物还在他们口中的时候,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
神的怒气就向他们上腾, 杀了他们内中的肥壮人, 打倒以色列的少年人。
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
虽是这样,他们仍旧犯罪, 不信他奇妙的作为。
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
因此,他叫他们的日子全归虚空, 叫他们的年岁尽属惊恐。
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
他杀他们的时候,他们才求问他, 回心转意,切切地寻求 神。
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
他们也追念 神是他们的磐石, 至高的 神是他们的救赎主。
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
他们却用口谄媚他, 用舌向他说谎。
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
因他们的心向他不正, 在他的约上也不忠心。
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
但他有怜悯, 赦免他们的罪孽, 不灭绝他们, 而且屡次消他的怒气, 不发尽他的忿怒。
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
他想到他们不过是血气, 是一阵去而不返的风。
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
他们在旷野悖逆他, 在荒地叫他担忧,何其多呢!
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
他们再三试探 神, 惹动以色列的圣者。
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
他们不追念他的能力 和赎他们脱离敌人的日子;
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
他怎样在埃及地显神迹, 在琐安田显奇事,
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
把他们的江河并河汊的水都变为血, 使他们不能喝。
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
他叫苍蝇成群落在他们当中,嘬尽他们, 又叫青蛙灭了他们,
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
把他们的土产交给蚂蚱, 把他们辛苦得来的交给蝗虫。
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
他降冰雹打坏他们的葡萄树, 下严霜打坏他们的桑树,
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
又把他们的牲畜交给冰雹, 把他们的群畜交给闪电。
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
他使猛烈的怒气和忿怒、恼恨、苦难 成了一群降灾的使者,临到他们。
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
他为自己的怒气修平了路, 将他们交给瘟疫, 使他们死亡,
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
在埃及击杀一切长子, 在含的帐棚中击杀他们强壮时头生的。
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
他却领出自己的民如羊, 在旷野引他们如羊群。
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
他领他们稳稳妥妥地,使他们不致害怕; 海却淹没他们的仇敌。
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
他带他们到自己圣地的边界, 到他右手所得的这山地。
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
他在他们面前赶出外邦人, 用绳子将外邦的地量给他们为业, 叫以色列支派的人住在他们的帐棚里。
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
他们仍旧试探、悖逆至高的 神, 不守他的法度,
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
反倒退后,行诡诈,像他们的祖宗一样; 他们改变,如同翻背的弓。
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
因他们的邱坛惹了他的怒气; 因他们雕刻的偶像触动他的愤恨。
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
神听见就发怒, 极其憎恶以色列人。
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
甚至他离弃示罗的帐幕, 就是他在人间所搭的帐棚;
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
又将他的约柜交与人掳去, 将他的荣耀交在敌人手中;
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
并将他的百姓交与刀剑, 向他的产业发怒。
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
少年人被火烧灭; 处女也无喜歌。
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
祭司倒在刀下, 寡妇却不哀哭。
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
那时,主像世人睡醒, 像勇士饮酒呼喊。
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
他就打退了他的敌人, 叫他们永蒙羞辱;
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
并且他弃掉约瑟的帐棚, 不拣选以法莲支派,
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
却拣选犹大支派—他所喜爱的锡安山;
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
盖造他的圣所,好像高峰, 又像他建立永存之地;
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
又拣选他的仆人大卫, 从羊圈中将他召来,
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
叫他不再跟从那些带奶的母羊, 为要牧养自己的百姓雅各 和自己的产业以色列。
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
于是,他按心中的纯正牧养他们, 用手中的巧妙引导他们。