< Zabura 78 >
1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
阿撒夫的訓誨歌。 我的百姓,請傾聽我的指教。請您們側耳,聽我口的訓導。
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
我要開口講述譬喻,我要說出古代謎語。
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
凡我們所聽見所知道的,我們祖先傳報給我們的,
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
我們不願隱瞞他們的子孫;要將上主的光榮和威能,他所施展的奇蹟和異行,都要 傳報給後代的眾生。
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
他曾在雅各伯頒佈了誡命,也曾在以色列立定了法令;凡他吩咐我們祖先的事情,都要一一告知自己的子孫,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
叫那未來的一代也要明悉,他們生長後,也要告知後裔,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
叫他們仰望天主,不忘記他的工行,反而常要遵守天主的誡命,
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
免得他們像他們的祖先,成為頑固背命的世代,成為意志薄弱不堅,而心神不忠於天主的世代。
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
厄弗辣因的子孫,雖知挽弓射箭,但是在作戰的時日,卻轉背逃竄。
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
他們沒有遵守同天主所立的盟約,他們更拒絕依照天主的法律生活。
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
又忘卻了天主的作為,和他顯給他們的奇事:
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
就是他昔日在埃及國和左罕地,當著他們祖先的面所行的奇蹟;
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
他分開了大海,領他們出險,他使海水壁立,像一道堤岸;
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
白天以雲柱領導他們,黑夜以火柱光照他們;
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
在曠野中,把岩石打破,水流如注,讓他們喝飽,
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
由岩石中湧出小河,引水流出相似江河。
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
但是,他們依舊作惡而得罪上主,在沙漠地區仍然冒犯至高之主。
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
他們在自己心內試探天主,要求滿足自己貪欲的食物;
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
並且出言反抗天主說:天主豈能設宴於沙漠?
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
他雖能擊石,使水湧出好似湍流;但豈能給人民備辦鮮肉與食物?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
天主聽到後,遂即大發憤怒,烈火燃起,要將雅各伯焚去,怒燄生出,要將以色列剷除;
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
因為他們不相信天主,也不肯依靠他的救助。
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
上主卻仍命令雲彩降下,開啟了天上的門閘,
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
給他們降下瑪納使他們有飯吃,此外給他們賞賜了天上的糧食。
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
天使的食糧,世人可以享受,他又賜下食物,使他們飽足。
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
他由高天激起了東風,以他的能力引出南風,
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
他們降下鮮肉多似微塵灰土,給他們降下飛禽,多似海岸沙數。
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
降落在他們軍營的中央,在他們帳幕的左右四方,
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
他們吃了,而且吃得十分飽飫,天主使他們的慾望得以滿足;
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
但他們的食慾還沒有完全滿足,當他們口中還銜著他們的食物,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
天主便對他們大發怒憤,殺死了他們肥壯的勇兵,擊倒了以色列的青年人。
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
雖然如此,他們仍然犯罪,還是不信他的奇妙作為。
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
他使他們的時日,迅速消逝,又使他們的歲月,猝然過去。
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
上主擊殺他們,他們即來尋覓上主,他們回心轉意,也熱切地尋求天主,
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
也想起天主是自己的磐石,至高者天主是自己的救主。
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
但是他們卻滿口欺騙,以舌頭向他說出謊言。
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
他們的心對他毫無誠意,不忠於與他所立的約誓。
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
但是他卻慈悲為懷,赦免罪污,沒有消滅他們,且常抑止憤怒;也未曾把自己全部怒火洩露。
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
他又想起他們不過是血肉,是一陣去而不復返的唏噓。
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
他們多少次在曠野裏觸犯了他,在沙漠中激怒了他,
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
三番五次試探了天主,侮辱了以色列的聖主。
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
不再想念他那有力的手臂,拯救他們脫離敵手的時日:
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
那日,他曾在埃及國顯了奇蹟,在左罕地行了異事。
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
血染了他們的江河與流溪,致使他們沒有了可飲的清水。
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
他使蠅蚋傷害他們,又使蛤蟆侵害他們。
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
把他們的產物交給蚱蜢,將他們的收穫餵給蝗虫。
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
下冰雹把他們的葡萄打碎,降寒霜把他們的桑樹打毀,
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
將他們的牲畜交給瘟疫,將他們的羊群交給毒疾。
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
向他們燃起憤怒之火,赫赫的震怒,以及災禍,好像侵害人們的群魔。
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
他為自己的憤怒開了路,未保存他們脫免於死途,瘟死了他們所有的牲畜,
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
擊殺了埃及所有的長子,將含帳幕內的頭胎殺死。
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
他如領羊一般地領出了自己的百姓,他在曠野中引領他們有如引領羊群。
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
領他們平安走過,使他們一無所畏。而海洋卻把他們的仇人完全淹斃。
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
引領他們進入自己的聖地,到自己右手所佔領的山區。
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
親自在他們的面前把異民逐散,將那地方以抽籤方式分為家產,讓以色列各族住進他們的帳幔。
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
但他們仍然試探和觸犯上主,沒有遵守至高者的法律,
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
叛逆失信,如同他們的祖先,徘徊歧途,好像邪曲的弓箭。
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
因他們的丘壇,招惹了上主的義憤,因他們的雕像,激起了上主的怒. 恨。
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
天主一聽到,即發憤怒,想將以色列完全擯除;
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
甚至他離棄了史羅的居處,就是他在人間所住的帳幕。
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
讓自己的力量為人俘擄,將自己的光榮交於敵手;
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
將自己的百姓交於刀劍,對自己的產業燃起怒燄。
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
烈火併吞了他們的青年,處女見不到婚嫁的喜宴;
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
他們的司祭喪身刀劍,他們的寡婦不能弔唁。
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
上主好似由睡夢中醒起,又好像酒後歡樂的勇士。
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
他由後方打擊自己的仇讎,使他們永永遠遠蒙羞受辱。
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
他並且棄捨了若瑟的帳幕,不再揀選厄弗辣因的家族。
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
但他卻把猶大的家族揀選;以及自己喜愛的熙雍聖山。
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
他建築了聖殿如天之高遠,永遠奠定了它如地之牢堅。
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
揀選了自己的僕人達味,且自羊圈裏選拔了達味。
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
上主召叫放羊時的達味,為牧放自己的百姓雅各伯,為牧放自己的人民以色列,
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
他以純潔的心牧養他們,他以明智的手領導了他們。