< Zabura 77 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Для дириґента хору. Для Єдуту́на. Псалом Асафів. Мій голос до Бога, — й я кли́кати буду, мій голос до Бога, — й почує мене!
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
В день недолі моєї шукаю я Господа, до Нього рука моя ви́тягнена вночі й не зомлі́є, не хоче душа моя бути поті́шена:
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
згадаю про Бога й зідха́ю, розважа́ю — й мій дух омліва́є! (Се́ла)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Ти де́ржиш пові́ки оче́й моїх, я побитий і не говорю́.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Пригадую я про дні давні, про роки відві́чні,
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
свою пісню вночі я прига́дую, говорю́ з своїм серцем, а мій дух розважа́є:
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Чи навіки покине Господь, і вже більш не вподо́бає?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Чи навіки спини́лася милість Його́? Чи скінчи́лося слово Його в рід і рід?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Чи Бог ми́лувати позабу́в? Чи гнівом замкнув Він Своє милосе́рдя? (Се́ла)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
І промовив був я: „То стражда́ння моє — переміна прави́ці Всевишнього“.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Пригада́ю я вчинки Господні, як чудо Твоє я згадаю відда́вна,
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
і буду я ду́мати про кожен Твій чин, і про вчинки Твої опові́м!
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Боже, — святая доро́га Твоя, котри́й бог великий, як Бог наш?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Ти Той Бог, що чу́да вчиняє, Ти ви́явив силу Свою між наро́дами,
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Ти ви́зволив люд Свій раме́ном, — синів Якова й Йо́сипа! (Се́ла)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Тебе бачили води, о Боже, Тебе бачили во́ди — й тремтіли, затряслися й безо́дні.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Лила́ся струмко́м вода з хмар, тучі ви́дали грім, тако́ж там і сям Твої стрі́ли літали.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
Гуркіт грому Твого на небесному колі, й блискавки́ освіти́ли вселе́нну, тремті́ла й трясла́ся земля!
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Через море доро́га Твоя, а сте́жка Твоя — через во́ди великі, і не видно було́ Твоїх стіп.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Ти прова́див наро́д Свій, немов ту ота́ру, рукою Мойсея та Ааро́на.