< Zabura 77 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
En Psalm Assaphs, för Jeduthun, till att föresjunga. Jag ropar med mine röst till Gud; till Gud ropar jag, och han hörer mig.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
Uti mine nöds tid söker jag Herran; min hand är om nattena uträckt, och håller intet upp; ty min själ vill sig icke trösta låta.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
När jag bedröfvad är, så tänker jag uppå Gud; när mitt hjerta i ångest är, så talar jag. (Sela)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Min ögon håller du, att de vaka. Jag är så vanmägtig, att jag icke tala kan.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Jag tänker uppå den gamla tiden, på de förra år.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Jag tänker om nattena på mitt strängaspel, och talar med mino hjerta; min ande ransakar.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Månn då Herren förkasta evinnerliga; och ingen nåd mer bevisa?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Är det så alldeles ute med hans godhet; och hafver tillsägelsen en ända?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Hafver då Gud förgätit att vara nådelig; och tillyckt sina barmhertighet för vredes skull? (Sela)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Men dock sade jag: Dermed qväl jag mig sjelf; den Högstas högra hand kan all ting förvandla.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Derföre tänker jag uppå Herrans gerningar; ja, jag tänker uppå din förra under;
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Och talar om all din verk, och säger om din anslag:
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Gud, din väg är helig; hvar är en så mägtig Gud, såsom du, Gud, äst?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Du äst den Gud, som under gör; du hafver bevisat dina magt ibland folken.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Du hafver förlossat ditt folk väldeliga, Jacobs barn och Josephs. (Sela)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Vattnen sågo dig, Gud, vattnen sågo dig, och ängslades; och djupen stormade.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
De tjocke skyar utgöto vatten; skyarna dundrade, och skotten foro deribland.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
Det dundrade i himmelen, ditt ljungande lyste på jordene; jorden rördes och bäfvade deraf.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Din väg var i hafvet, och din stig i stort vatten; och man fann dock intet din fotspår.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Du förde ditt folk, såsom en fårahjord, genom Mose och Aaron.