< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Estaba clamando a Dios con mi voz; a Dios clamé con mi voz, y él me escuchó.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
En el día de mi aflicción, mi corazón se volvió hacia el Señor: mi mano estaba extendida en la noche sin descanso; mi alma rehusaba ser consolada.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Mantendré a Dios en la memoria, con sonidos de dolor; mis pensamientos están turbados, y mi espíritu está vencido. (Selah)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Mantienes mis ojos del sueño; Estoy tan preocupado que no llegan las palabras.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Mis pensamientos se remontan a los días del pasado, a los años que ya pasaron.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
El recuerdo de mi canción vuelve a mí en la noche; y meditaba en mi corazón; mi espíritu se preguntaba.
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
¿El Señor me apartará para siempre? ¿Ya no será amable?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
¿Su misericordia se ha ido para siempre? tiene su palabra a nada?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
¿Ha olvidado Dios el recuerdo de su compasión? ¿Sus misericordias son cerradas por su ira? (Selah)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Y dije: Es un peso sobre mi espíritu; pero tendré en cuenta los años de la diestra del Altísimo.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Tendré en cuenta las obras de JAH: mantendré el recuerdo de tus maravillas pasadas.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Pensaré en todo tus obras. mientras mi mente repasa tus actos de poder.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Tu camino, oh Dios, es santo: ¿Que dios es tan grande como nuestro Dios?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Tú eres el Dios que hace obras de poder; has hecho clara tu fuerza para las naciones.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Con tu brazo has hecho libre a tu pueblo, los hijos de Jacob y José. (Selah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Te vieron las aguas, oh Dios; las aguas te vieron, tenían miedo; incluso el abismo estaba turbado.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Las nubes enviaron agua; los cielos emitían un sonido; y relámpagos por todas partes.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
La voz de tu trueno comenzó a rodar; el mundo estaba ardiendo con la luz de la tormenta; la tierra estaba temblando.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Tu camino estaba en el mar, y tu camino en las grandes aguas; no había conocimiento de tus pasos.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Estabas guiando a tu pueblo como un rebaño, por la mano de Moisés y Aarón.

< Zabura 77 >