< Zabura 77 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Начальнику хора Идифумова. Псалом Асафа. Глас мой к Богу, и я буду взывать; глас мой к Богу, и Он услышит меня.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
В день скорби моей ищу Господа; рука моя простерта ночью и не опускается; душа моя отказывается от утешения.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Вспоминаю о Боге и трепещу; помышляю, и изнемогает дух мой.
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Ты не даешь мне сомкнуть очей моих; я потрясен и не могу говорить.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Размышляю о днях древних, о летах веков минувших;
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
припоминаю песни мои в ночи, беседую с сердцем моим, и дух мой испытывает:
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
неужели навсегда отринул Господь, и не будет более благоволить?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
неужели навсегда престала милость Его, и пресеклось слово Его в род и род?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
неужели Бог забыл миловать? Неужели во гневе затворил щедроты Свои?
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
И сказал я: “вот мое горе - изменение десницы Всевышнего”.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Буду вспоминать о делах Господа; буду вспоминать о чудесах Твоих древних;
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
буду вникать во все дела Твои, размышлять о великих Твоих деяниях.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Боже! свят путь Твой. Кто Бог так великий, как Бог наш!
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Ты - Бог, творящий чудеса; Ты явил могущество Свое среди народов;
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Ты избавил мышцею народ Твой, сынов Иакова и Иосифа.
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
Видели Тебя, Боже, воды, видели Тебя воды и убоялись, и вострепетали бездны.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Облака изливали воды, тучи издавали гром, и стрелы Твои летали.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
Глас грома Твоего в круге небесном; молнии освещали вселенную; земля содрогалась и тряслась.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Путь Твой в море, и стезя Твоя в водах великих, и следы Твои неведомы.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Как стадо, вел Ты народ Твой рукою Моисея и Аарона.