< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
Para o músico chefe. Para Jeduthun. Um Salmo por Asaph. Meu grito vai para Deus! De fato, eu clamo a Deus por ajuda, e para que ele me ouvisse.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
No dia do meu problema, eu procurei o Senhor. Minha mão estava estendida durante a noite, e não me cansava. Minha alma se recusou a ser consolada.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
Eu me lembro de Deus, e eu gemo. Eu me queixo, e meu espírito está dominado. (Selah)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
Você mantém minhas pálpebras abertas. Estou tão perturbado que não posso falar.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
Eu considerei os dias de antigamente, os anos dos tempos antigos.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
Lembro-me de minha canção durante a noite. Considero em meu próprio coração; meu espírito inquire diligentemente:
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
“Será que o Senhor nos rejeitará para sempre? Será que ele não será mais favorável?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Sua bondade amorosa desapareceu para sempre? Sua promessa falha por gerações?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Será que Deus esqueceu de ser gracioso? Será que ele, com raiva, reteve sua compaixão”? (Selah)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
Then Eu pensei: “Vou apelar para isso: os anos da mão direita do Altíssimo”.
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
Lembrar-me-ei dos atos de Yah; pois vou me lembrar de suas maravilhas de outrora.
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
Também vou meditar sobre todo o seu trabalho, e considere seus atos.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
Seu caminho, Deus, está no santuário. Que deus é grande como Deus?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
Você é o Deus que faz maravilhas. Você deu a conhecer sua força entre os povos.
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
Você resgatou seu povo com seu braço, os filhos de Jacob e José. (Selah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
As águas o viram, Deus. As águas o viram, e eles escreveram. As profundidades também são convulsionadas.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
As nuvens derramaram água. Os céus ressoavam com trovões. Suas setas também piscaram ao redor.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
A voz de seu trovão estava no redemoinho. Os relâmpagos iluminaram o mundo. A terra tremeu e sacudiu.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Seu caminho foi através do mar, seus caminhos através das grandes águas. Seus passos não eram conhecidos.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
Você liderou seu povo como um rebanho, pela mão de Moisés e Arão.

< Zabura 77 >